Saturday, February 5, 2022

Tun Ina Karama 7 to 10


readerglobe.com.ng


Page 7

               ASALIN LABARIN

Waye yusuf Bashir mado kankiya? Alhaji Bashir mado kankiya haifafan cikin garin kankiya ne dake jahar katsina Alhaji bashir su hudu ne wurin mahaifinsu. Alhaji bashir shine babba a cikin su da shi da kanin sa Alhaji bello sai kanwar su hajiya mariya Salina autar su rabi atu, sun taso cikin jin dadi da walwala ta rayuwa, sakamakon mahaifinsu yana da ilimi na addini dana zamani yasa yazama wayayye kuma gashi yana amfani da iliminsa wurin iya mu amula da mutane, sannan ga tarin dukiya Allah ya hore masa, yana kasuwancin shi cikin ilimi da gogewa ta rayuwa, matar shi daya hajiya hauwa'u wadda itace mahaifiyar su Alhaji bashir, sunyi auren soyayya da Alhaji mado itama yar cikin garin kankiya ce. sunyi zama na soyayya da Alhaji mado wanda har Allah ya azurta su da haihuwar yara guda hudu, shima Alhaji bashir koda yake dan boko to ya biyo baban shi wurin son business sosai don tunda ya taso ya gama karatunsa na degree akan business ne yayi karatu har master's din shi.













Shi kuma Alhaji bello gaskiya yafi karfi a govment saboda yanzu haka shine commissioner na manoma watau agric.ita kuma hajiya mariya sakamakon mijinta mai haline yana da tarin dukiya sosai shiyasa ita bata aiki sai kawai ta fada harkar kasuwanci, tana fita dubai tana kawo kaya sosai.sai Rabi'atu wadda itama tayi aure amma tana aiki da ma'ikatar lafiya ta kano, gaba dayansu kowa yana da rufin asiri daidai gwargwado saboda Alhaji moda koda yake da kudi bai yarda ya bar yaranshi ba babu ilimin addini dana zamani ba, bayan rasuwar maifinsu ne Alhaji mado Alhaji bashir ya koma katsina da zama a inada ya auri diyar aminin babansu Alhaji garba mai dala, wadda dama suna soyayya dashi wadda hakan yasa iyayensu sukayi masu alkawarin auren junan su kuma Allah ya kaddara

Shikuma Alhaji bashir dalilin dayasa ya koma katsina da zama saboda duk harkokin mahaifin shi suna can to koda ya rasu sai ya tattara gaba daya ya koma da zama, yaso ya tafi da mahaifiyasu amma ta nuna mashi tafi son zamanta anan kankiya cikin danginta haka nan ya hakura badon ranshi yaso ba, amma duk satin dunya yana zuwa ya kwana biyu wurin mahaifiyarsa saidai idan baya kasar, kuma yana zuwa da matarsa hajiya khadija wadda mace ce mai karamci da nuna kulawa ga yan uwan mijinta shiyasa ta shiga ran kowa na family dinsu Alhaji bashir, ita kanta hajiya hauwa'u tana kaunar sirikar tata sosai bata son taji ance ga laifinta, shikuma Alhaji bashir ganin yanda take kula da mahaifiyarsa da yan uwansa yasa yake kara ganin darajarta da kimarta.

Kuma yake kyautata mata, itama haka zamansu yake cikin mutunci da girmama juna, to amma duk da haka basa shiri da hajiya mariya saboda ita gaskiya halinta ya sha banban yan uwanta, ita mace ce wadda tasa duniya gaba bata tunanin komi sai son zuciya, saboda tana fita kasashe tana haduwa da kawaye sun zugata tana ganin kowa ma bai isa ba, saboda haka ne basa shiri da Alhaji bashir yayanta shikam duk harkar wani shashanci baya cikinta, kuma shi mijin nata saboda son dayake yi mata baya iya magana duk yanda take so to haka za ayi Allah ya kyauta,itama mijinta dan katsina ne nan suke zaune a le out, shima Alhaji bello yana katsina tare da iyalinsa, sai hajiya rabi'atu   dake aure a kano ita mijinta dan kano ne a nan kundila suke da zama anan take aikinta a ma'katar lafiya dake jaha.













Allah ya Albarkaci Alhaji bashir da haihuwar yara uku aunty zainab ce babba sai yusuf sai kuma Nafisa wadda itace auta, rayuwar farin ciki da kaunar junan su haka rayuwa take tafiya, hajiya khadija su uku ne wurin mahaifinsu Alhaji suleman shine babba sai ita umma sai kuma babana wanda shine kaninta Alhaji mansir shine mahaifina Allah yayi masa rasuwa ne a sakamakon hadarin mota, daga kaduna zuwa katsina, Allah ya gafarta ma iyayenmu yasa Aljannace makoma Ameen ya hayyu ya qayyum.

To lokacin mahaifina shi yana kaduna ne zaune tunda can yake aiki tare da mahaifiyata wadda dama it yar kaduna ce anan ya aureta a lokacin daya rasu an haife ni amma shekareta daya lokacin, saboda haka iyakar zaman danayi da mahaifiyata kenan ana yayeni hajiya khadija tace lallai sai an badani haka dai mamana tayi kawai ci saboda karamcin yayar mijin nata ta hakura ta bada ni haka na tashi ina ganin umma itace mahaifiyata tunda koda wasa bansan umma da Abba ba basune iyayena ba tunda ko yaransu ban taba ji abakinsu ba kowa yana sona, nasan dai akwai mamin kaduna tunda haka naji suna ce ma mamana, kuma sai inji suna ce mata mamin yusuf naga kuma yawancin zaman shi acan wurinta ne .na tambaya umma sai tace mani ai ita mami itace mamanshi dana dameta da tambaya sai tace tashi kibani wuri harga Allah ban kawo komi araina ba, mami tayi aure ta auri wani aminin dad dina wanda shima matarsa wurin haihuwa ta rasu shima mutumin kirkine, amma mami da kyar ta amince da auren shi dayake kuma Allah ya kaddara  haka ta auri Alhaji isma'il shima dan zaria ne amma engineer ne yanzu haka yana Abuja can yake aiki amma nan yabar mami a kaduna saboda tace tafi son zaman kata anan tare da yaranta saidai yarinka zuwa weekend ko kuma wani lokaci suje su danyi hutu su dawo.












Diyarshi wadda matarshi tabari itace babba wurin mami sai wadanda ta haifa guda uku yaran shi hudu amma baka cewa mami ta haifi ummi ba  sai Abdul da khalid da halimatu sune yaran mami Hajiya mariya yaranta biyu jamilace babba sai kanwarta nabila sakamakon tsada haihuwa datayi wai ita bata son ta tara yara kuma su tsaida mata harkokinta nabila ba halinsu daya ba da jamila shiyasa gaba daya basa shiri  shiyasa koda yaushe tana gidan umma muna tare ita kuma hajiya mariya ta tsani hakan shiyasa ko hidima akaje ta rinka yima umma habaici kenan ita kuma bata kulata.

Page 8

Yaya yusuf da umar cousins ne saboda umar shine babba wurin Alhaji bello kanin Alhaji bashir baban yusuf, tare suka taso tun suna yara babu abunda ke raba su sai in yazama dole, ko karatunsu tare sukayi shi india couse dinsu ne ba daya ba shi yusuf permacy ya karanta shi kuma umar Account ne, duk da haka dasuka dawo gida nigeria suna tare a company daya wanda dama na su ne company babu abunda akeyi cikin shi sai hidimar magunguna sakamakon dama abunda yusuf ya karanta kenan, kuma suna samun kwangila daga gwamnati saboda babu kasar da basu kawo magani kuma masu inganci basu yarda su hada hulda da kasashen da suke yaudarar kasarsu saboda kishin kasa.

Jamila tare suka taso don itama dakadan suka girmeta ko a skul shekara daya ce tsakaninsu da ita itama india tayi karatu tare da su yusuf amma ita kwararra likita ce yanzu haka tana cikin likitocin da ake ji dasu a cikin jihar katsina tana aiki ne da fedaral medical center dake cikin garin katsina, jamila tana son yusuf sosai arayuwarta sbd irin mazan da mace zatayi alfahari dasune, kuma tanada wani hali duk abunda take so to bata  boyewa ko jin kunyar nuna mashi kuma tana da son kanta da yawa da son zuciya kamar yadda ta gani wurin uwarta Nidai na taso hannun ummatah da Abbanah wanda su nake ma kallon iyayena da suka haifeni, saboda karamci irin na dangin mamana tunda ko su ban taba jin sunce wani abu ba na dangane dani kawai dai abunda nafara fahimta ina dan kama da mamin kaduna amma bana sawa araina akwai wani abu kuma ina jin ina son matar sosai araina amma tunani nako don tana mahai fiyar yaya yusuf ne.na tashi cikin so da soyayyar yan uwana su aunty zainab.












Haka nayi krtuna primary da secondary anan katsina lokacin dana gama secondary ne ina da shekara 17 kuma ashekarar akayi mani aure da yaya yusuf wanda dama wai jirana kawai yakeyi saboda duk matan dake bibiyarsa baya ma kula su ciki ko harda jamila, bai so maganar aurena yanzu ba amma hakan bata samu ba.

Saboda yaso ace na fara jami'a kwatsam sai gashi ya canza shawara saboda wani dalili nashi, hakan yasa aka gaggauta yin auren mu. Bana manta wannan ranar da akayi bikin wata cousing dinmu Aisha wanda aranar ne ne komi ya canza a sakamakon wani hoto da da jamila ta hada tare da wani saurayi ta turo ma yusuf shi kuma lokacin yana gida.abunda ya faru, mun shirya nida nabila kanwar jamila zamuje wurin dinner to dama gaskiya itace kawata sai na nafisa autarsu yusuf tunda duk kanmu daya kuma mun shaku da juna sosai, to nafisa tana wurin aunty zainab a Abuja, mun gama shiryawa muka fito daga dakina muka samu ummah tana zaune tana kallon tashar sunnah tv tana ganinmu ta fadada murmushinta cikin kulawa tace masha Allah kunyi kyau yan matana cikin jin kunya muka rufe fuska tare da isowa kusa da ita muka zauna gefen ta muka sata tsakiya, cikin shagwaba wadda tariga ta zame mani jiki nace ummatah ina yayana? tare da kallon kofar da zata sadaka da sashin shi cikin kulawa tace yaje masallaci amma naga alamar kamar ba zai fita ba, yanzu dai bari in sanar ma Adamu driver ya kaiku tana magana tana kallon wayarta dake caji kafin tayi ta kara mgn na mike na dauko wayar na mika mata, bugu daya ya dauka ta sheda masa abunda zaiyi ya amsa da to hajiya mikewa mukayi tare da yi mata sallama tace kada mu wuce karfe tara komi mukeyi insha Allahu muka ce tare da fita waje muna fita muka ga Adamu yana kokarin fiddo wata katuwar jeep prado blue sai shaning takeyi  har inda muka tsaya ya iso ya bude mana muka shiga baya muka zauna tare da gashe shi ya amsa mana cikin walwala baba mai gadi ya bude mana muka fita sai liyafa place inda akeyin dinner .

Fitarmu kenan shikum yusuf ya fito daga masallacin kofar gidanmu yana fitowa ya hangi motar gidanmu ta fita daga get cikin mamaki yace to wa yafita yanzu a wannan motar? cikin hanzari ya shiga cikin get din gidan tare da sallam baba mai gadi ya amsa kafin yace komi yusuf yace baba waya fita da mota yanzu cikin mutunci yace ai yallabai Adamu ne hjy tace yaje ya kaisu autarta wurin biki da yake duk ma aikatan gidan haka suke kira na da autar hajiya, ok kawai yace ya shige cikin gidan tare da sallama umma ta dago kai tare da amsa masa sallamar babu walwala a fuskarsa ya zauna kusa da umma yace umma saida kika bar yaran nan suka tafi wurin dinner nan ko? "Yes tace ai banyi tunanin zasu dade ba kasan hawwa ma da ba son hayaniya ne da ita ba, ai umma da kin kinkirani saboda darene kuma kin san jamila zataje tana iya yima su hauka tunda sakarai ce cikin damuwa ya karashe mgnar."tace ba komi insha Allahu lafiya zasu dawo amma duk da haka shirya ka dawo da su saikace ma Adamu ya taho gida "ok yace tare da mikewa zuwa dakin sa ya canza kaya tunda dama kafin yaje masallaci yayi wanka, yana shiga ya shirya cikin kananan kaya wanda sun karbi jikinsa yayi kyau sosai yana shiri ya na kallon agogon dake manne a dakin, ya dauko perfumes yana fesawa wayar shi tayi kara alamar text ya shigo da kuma hasken da wayar ta karayi, kamar bazai duba ba kuma kawai sai yaji yana son ya duba koda ya dauki wayar sai yaga ashe sako ma na whatsapp ne kuma sunan jamila ne ke yawo akan sakon kamar zai aje wayar sai kuma yayi tsaki miss ya bude sakon.











Innalillahi wa'innailaihin raju'un, haka kawai yake maimaitawa.sakamakon wasu hotona da jamila ta tura mashi na hawwa tare da wani saurayi kamar suna mgn ita kuma hawwa tana dariya wanda ita bama tasan saurayin yana kusa da ita haka ba.

Jikin shi har rawa yakeyi yasa hannu ya dauki key din motar shi a sukwane ya fiti pallow babu umma hakan ya bashi damar fita kawai inda yayi parking ya nufa ya shiga motar a rude sbd tsabar kishi, baba mai gadi ya bude mashi get tare da daga masa hannu adawo lafiya yace, haba ina ko ji bayayi haka ya fita cikin tashin hankaki da rikicewa hoton hawwa kawai yake gani tana yima saurayin nan dariya, hawwa kina son feedback me nayi maki?

Page 9

Haka yaketa maimaitawa yana tuki amma gaba daya hankalin shi yana wurin wannan hoto, cikin minti kalilan ya isa liyafa place haka ya shiga ciki, daidai inda motar Adamu driver take yayi parking, cikin hanzari  Adamu ya fito yana karasawa wurin shi  lokacin da ya bude mota ya fito hannuwan shi cikin aljihun wandon shi, duk dayake cikin bacin rai ba karamin kyau yayi ba, Adamu yace yallabai barka da isowa, yauwa kawai yace atakaice, ina suke? ya tambaya shi "ai suna ciki ranka shi dade bai rufe baki ba saiga hawwa ta fito daga hall din tana neman nabila don ta gaji tana so tafi gida haka nan, daidai inda motar su take ta hango Adamu shida yaya yusuf, cikin faduwar gaba ta ambaci yaya yusuf kuma anan? cikin sauri ta nufi wurinsu inda tunda ta fito suka hangota saboda hasken fitilun dake wurin. Adamu ne ya katse shirunsu da cewa gama autar hajiya nan isowa.













Yanda taga alamunshi, tasan akwai matsala haka ta karasa jiki ba kwari cikin tsoro tace yaya kaine?" Shiga mota kawai yace mata"yaya nabila kafin ta karasa ya daka mata tsawa! wanda har Adamu saida ya firgita"shiga mota ya sake cewa cikin rudewa ta bude motar ta shiga, ya juyo yace m Adamu kajira nabila ka taho da ita. cikin girmamawa ya amsa da to yallabai, a fusace ya isa wurin motarsa ya bude ya shiga ya fita a180_200 ran maza ya baci to hawwa ina tausaya maki hannun yusuf Adamu mamaki kawai ya hanashi motsi har na tsawon minti biyu atsaye sannan ya juya ya koma wurin motarsa cike da tunanin mai ya bata ma oga rai haka? to koma menene Allah ya kyauta.

Duk abun nan dake faruwa tsakanin yusuf da hawwa, su jamila na kallonsu tana cikin motarta  inda tayi parking suna zaune itada kawarta dama suna jiran ganin shigowar yusuf saboda ba kowa zai lura da ita ba a inda tayi parking suna zaune ita da kawarta samira wanda dama samira ce ta shiga ta dauko wannan hoto wanda shi kanshi wanda ta hada tayi masu hoton baima san tanayi ba har tagama kulla sharrinta ta fito, motad yusuf na fita daga get din suka tafa ita da samira suka kyalkyale da dariyar mugunta"jamila tace yau na fara dasa masu tashin hankali atsakaninsu ke nan kinga yanda dai ya fusata gashi dama akwai zuciya kuma na lura irin mazan nan ne masu kishi  kinga tunani da yawa zaiyi akanta yarinka ganin dama tana kula maza awaje "yes samira tace wannan haka yake cikin dariya samira tace to yanzu me kike ganin zaiyi mata? "jamila tayi murmushin mugunta tace ubanta zaici kawai.

Ke bakiga yanda ya fusata ba"hakane amma baki ganin mamanshi zata taka mashi burki akan hakan tunda dama kince bata son abunda zai taba yarinyar samira ta tambaya jamila."kada ki damu kawata shine dalilina na bata alkarsu saboda uwarshi ta dauki burin duniya ta dora ma wannan shegiyar yarinya wallahi na tsaneta mtsss nasan zata fusata da zaran mata wani abu kuma kinga daga nan sai abubuwa su fara canzawa nikuma  a lokacin zan fara game dina wanda duk families dinmu zasu san muna tare da juna wallahi  samira zan iya aiwatar da komi akan yusuf dalilin i love her with all my heart: ok kawata komi zaiyi dai dai don ma mommy bata kasar amma komi zai zama normal"samira ta jinjina kai alamar gamsuwa da maganar kawartata."jamila tace mu wuce ko?"samira ta amsa mata da yes, haka suka tashi mota suka fita dama abunda ya kawo su kenan kuma sun ai watar zuciyarsu wasai saura suji feedback.

Nabila ta duba bataga hawwa ba kuma ga wayarta a hannun ta bare ta kirata, haka ta yanke shawarar fita waje don tasan haww ba hayaniya take so ba, tana fitowa tayi wurin da Adamu driver yayi parking yana kwance a mota yana jiranta kwankwasa gilas din motar tayi ya tashi tare da bude gilas din yana tambayarta nabila kin gamane?eh ta amsa masa tare da tambayar shi hawwa bata fito bane?"ai yanzu ba dadewa yallabai yazo suka tafi .cikin razana tace yaya yusuf yazo nan lfafiya dai ko?walhi bansani ba amma dai naga ranshi a bace yake, "ta jinjina kai tace Allah dai yasa lafiya" Amin ya amsa mata ta bude motar ta shiga ya ja suka tafi cike da tunanin me ya faru aranta.














Hankali atashe yake tafiya da mota saboda gudu kawai yakeyi kamar zai bar gari .nidai jikina rawa kawai yakeyi zuciyata na bugawa tunda nashiga motar kafin mu shiga unguwar mu naga ya gangare gefen titi yayi parking, cikin razana na dago kaina da nufin yin magana "waye shi? naji yace, cikin rashin fahimta bansan abunda kake nufi ba" ki fada mani tsawon wane lokaci kuke tare shi? yakara tambaya, "wallahi yaya bansan abunda kake nufi ba. juyowa yayi cikin tsawa! yace shut up! my friend ki sanar dani alakarki da shi tun kafin ranki ya baci! bansan lokacin da kuka ya kufce nani ba nace ni bansan komi ba amma kaki yarda." ok kawai yace tare da jefo mani wayar shi akan cinyata duba kigani tunda nasa ba yi maki karya, cikin sauri na dauki wayar tare da ganin wani pic nawa da wani saurayi kamar muna magana ina dariya.

Page 10

Cikin sauri na dauki wayar nice zahiri ba karya amma ban san wanene wanda yake kusa dani ba har ina dariya nasan dai fatima kawata nake magana da ita a lokacin amma ya akayi wannan mutumin kusa dani haka, na shiga uku! an bata ambata wallahi yaya ban san shiba asalima nasan na tsaya wurin nan amma bada shi nake maganaba amma ban sanshi ba yaya cikin kuka na karashe maganata tare da jin wani zafi a zuciyata "tunda nafara magana yake kallona yaso ya gasgata maganata amma kishi ya hana yaga hakan tare dani." Ok bani wayata na mika mashi zan kara magana ya daga mani hannu sbd gaba daya kukan da nakeyi har cikin ranshi yake jin shi. kamar bashi yayi maganar ba naji yace hawwa aure kike so?cikin sauri na girgiza kai alamar a'a to ko ba kiso yazama dole saboda bazan iya wadannan abubuwan"walhi yaya banida saurayi bare ince ina son aure to wazan aura.

Bayan nasan bani da kowa kuma karatu nake buri, na cigaba da cewa duk wanda yayi mani sharri bazan yafe masa ba tunda ban aikataba, "batare daya kalleni ba ya tada mota tare da cewa ki cigaba da shirye shiryen aurenki nan da lokacin kankani insha Allahu, wayyo Allah! nace shikan shi saida ya tsorata a fusace yace kika kara yi mani ihu amota sai na fasa baki.nasa hannu na toshe bakina, ya figi mota muka karasa cikin unguwarmu.muna isa gida cikin get din gidanmu, tun kafin ya gama parking na balle marfin mota na shiga gida da gudu tare sakin kuka mai karfi ummace tare da nabila suna maganar to ina muka tsaya ba iso ba.













Ba " nabila tace ma umma Adamu yace rai bace yaya yazo cikin mamaki  tace to koma menene ai sai  ya dawo mani da ita gida ko, bata rufe baki ba na fado falon da kuga gaba daya juyo sukayi cikin mamaki suna tambayar ta me yafaru? cikin kuka nace umma kada kibari yaya ya fadi Abbanah ina son aure na hade hannuwa na alamar rokonta.cikin rashin fahimtar maganata ta zaunar dani kan kujera  nabila kuma ta zauna gefena tare da rike hannuna "umma tace wai meke faruwa? waye baki so kuma?" Yusuf ne ya shigo tare da sallama amma fuskar nan tashi babu annuri sai ji sukayi yace dama kin daina kuka ki fara shirin aurenki."cikin daga murya umma tace wace by irin mgn kakeyi yusuf? me ya faru ne?"umma ki tambaya ta abunda tayi dama ni nace abarta ta fara jami'a to yanzu ra'ayina ya canza zan jira dawowar Abbah tunda ya fara magana umma ke kallonsa tana nazarin irin soyayyar hawwa tsantsa a idon shi da kishin ta cikin kauda kai umma tace baka isa ba yusuf  babu wanda zai takurata da mgnr aure"amma umma ya kamata ki saurareni mana"cikin tsawa tace banda lokaci saurarenka  zai kara mgn ta daga masa hannu tare da cewa ya isa haka bai kara magana ba ya nufi sashensa  yana jin wani zafi a zuciyarsa ta juyo tace na nabila tashi ku shiga daki ku kwanta.

contac-form

Labels:

0 Comments:

Post a Comment

Subscribe to Post Comments [Atom]

<< Home