Tun Ina Karama 11to 12
TUN INA KARAMA
Page 11
Tunanin kawai yakeyi aransa ina zai samu mafita? yasan dai umma ba sauraren, gaskiya dana bi shawarar Abba dayace in fito ayi mani aure da hawwa da haka bata faru ba gashi tun ba'aje ko ina ba abubuwa na shirin lalacewa, naso in barta ta fara karatu domin ta kara samun wayewa ne amma kash, kishinta bazai barni ba ina sonta itace mace ta farko dana ke jinta araina amma bata sani ba ina ganin tayi kankanta da zan nuna mata wacece ita agareni.don har yanzu kallon dan uwanta takeyi mani na jini ba wai ta fahimci sona take ba, gaskiya nayi kuskure yakamata hawwa ta san tun tana karama nake dakon sonta.
Haka muka tashi da asuba mukayi sallah da addu'oin mu tare da tilawar alkur'ni mai girma, wanda dama mun saba saida gari ya fara wayewa muka tashi, na kalli nabila nace mata sister zan dan koma in kwanta don kaina ke dan ciwa ok ba damuwa tace ki kwanta ki huta ni zanje in taya Asabe break, to shikenan nace na koma na kwanta.nabila tana shiga sashen umma ta shiga dakin tare da sallama, umma tana hada wasu kaya da zatayi amfani dasu ta juyo ta amsa ma nabila sallam cikin fara' da kulawa nabila har kasa ta tsugunna ta gaishe da umma bayan sun gama gaisawa na ta tambaya hawwa ko lafiya nabila ta amsa da bacci ne ta koma ta kwanta"umma tace to ba damuwa kema ki koma ki kwanta mana a a ummah zan taya Asabe ne break to shikenan ki sameta kichen din, yaya yusuf koda ya tashi da asuba yaje masallaci ya dawo ya gama abunda yakeyi ya shirya tsab tunda ya gama yanke hukuncin tafiya wurin mami kaduna, bayan ya gama ne ya fito ya wuce part din ummah ya shiga dakinta tare da sallama ta amsa masa ba yabo ba fallasa bayan sun gaisa ne yake sheda mata tafiyar da zaiyi kaduna, hmmm kawai tace tare da fadin Allah ya tsare hanya yasa a adawo lafiya.
Yusuf ya sauke ajiyar zuciya tare da kallon agogon hannunsa yace yakamata mu wuce ko?"umar ya daga kai alamar eh haka suka fito daga part din umar inada suka samu Ammi a falon gidan su umar suka gaisheta cikin girmamawa Ammi tace yusuf yasu hajaya ya amsa da lafiya klau Ammi "to masha Allah Allah ya taimaka suka amsa da Amin suka mike tsaye zasu tafi umar yace Ammi zamuje kaduna sai yanda ta yiwu to ba komi Allah yasa adawo lafiya amin suka amsa suka fita tabi su da kallo tana jin dadin alakarsu sosai haka suka shiga motarsu suka fita umar na tuki sai kaduna garin gwamna sai muce Allah yasa a dace yusuf.
Bayan na tashi wurin karfe 10:30 sbd babu wanda ya tasheni saka makon umma tace abarni in huta, ina tashi da addu'a bakina tare da salati na mike na shiga toleit bayi wanka na fito na shafa mai ajikina tare da spray masu dadi ina cikin bude drawer ne in dauko rigar da zan sanya sai wata leda ta fado ina kai hannuna zan dauka gabana ya yanke ya fadi cikin sauri naje wurin window na yaye labulan inda yake parking babu motarsa ya salam!ina ka tafi bayan kace yau zamu bude wannan ledar yaya? why kayi avoiding me?
To fa yanzu aka fara wasan fa menene burin jamila yaya hawwa zata dauki aurenta da yusuf? wace irin kalubale ke tare da rayuwarsu? to koma me kenan mujira dawowar Abba, nagode da kauna masu biyoni a picture suna nuna mani soyayyarsu da littafina mai suna tun ina karama insha Allahu nima ina akai aku don jin dadinku.
Page 12
Ban san lakacin da hawaye suka zubo mani ba nayi sauri na nasaki labulen na koma wurin drawer na maida ledar da ban san menene ciki ba nace nima bazan bude ba har sai idan ya daina fushi dani haka na shirya cikin doguwar rigata ja mai stone agaban ta na dauki vell dinta na saka powder kawai nasa batare danayi make up ba haka na sanya takalmina simple na fito nasame su su duka gidan suna falo ummah da Asabe da nabila Asabe mai aikinmu ce amma mun dauketa kamar kaka saboda shakuwa dakuma kirkin matar shiyasa ta zama tamkar yar uwa ta jini da yanda ta dauki umma shiyasa umma ta jata ajikinta sosai gani na kowa da murmushi a fuskarsa umma ko cikin ranta cewa tayi masha Allah yayi hallita wurin please yusuf ya tashi hankalinsa don hawwa mace ce kyaunta yanzu yake kara fitowa sosai isowa nayi na zauna kusa da ummah na dora kaina bisa kafadarta shi ya dawo da ita tunaninta nace ummatah ina kwana lafiya klau ta amsa tare da cewa ya ciwon kan naki ya bar ciwo ko?na amsa da eh ummatah ya bar ciwon kafin mu kara magana nabila tace ai sai ki tashi kije kiyi break kike ta wani shishigema ummah na dan harareta to yar sa ido.Dariya su ummah sukayi mana na kalli Asabe nace kakas ina kwana daftn dai kinyi mani kunun gyada kwarai kuwa autar hajiya nayi maki , "ummah ta kalleni cikin kulawa tace tashi kije daning kiyi break dinki ke dai dama ya rage na amsa to tare da mikewa tsaye na nufi daning ina zama na zuba abunda zanci na gama na dawo cikinsu hira sukeyi ina jefa nasu baki jefi jefi amma bawai don ina fahimtarsu ba hankalina gaba daya yana wurin yaya yusuf tunda ya saba mani idan har zai fita bai ganni ba to zaiyi mani text " kamar haka sleeping girl in kin tashi ki nemi yayanki yana son jin muryar littel din gidan su.
Ya jinjina kai alamar yes, umar yayi dariya bai dai ce komi ba, reply ya bata kamar haka. (sorry littel sister ummanki tana sonki da yawa bazata bari in rinka fahimtar dake gaskiya ba don haka nina tafi kaduna wurin mamita sai Abba ya dawo zan dawo gidanku an good luck all ur best littel i miss you too) idona lumshe kamar mai bacci naji shigowar sako cikin hanzari na bude amma abunda nagani ne yasani mikewa tsaye tare da fadin what! da karfi na fashe da kuka cin ta shin hankali kowa ya ya taso gareni walhi umma kadunanan bazan zauna ba nima yaya yace ba zai dawoba nima can zan koma ya za'ayi a rabani dashi umma ya zaki barshi yabar gidanmu baki hana shi tafiya ba, tunda na fara magana cikin kuka kowa kallona yakeyi suna ma kasa cewa komi, nabila ce ta matso ta dafani tace wai hawwa me ya farune haka? ki sakeni nabila nima binshi zanyi umma bata sona tunda har ta barshi ya tafi wayyo Allah zan mutu, ran umma yayi mugun baci da jin kalamin dake fitowa daga bakina hankalinta ya tashi wai bata sona yau ita hawwa take fadi ma haka lallai dole ta koya mata hankali don gaba.bata san lkcn da ta daga hannu ba ta dauketa da mari ba ta sake dauke ta da mari akaro na biyu, kowa na wurin saida suka tsorata ni ko wata juwa nagani tana dibana wanna shine tarihin arayuwata wanda umma ta dora hannunta akaina.
Umma tace Allah yasa Amin suka amsa gaba daya shi kam yusuf yana gama tura mata text din ya kashe wayar shi cikin hikima ya amshi wayar umar shima ya kasheta batare da umar ya fahimta ba, koda suka shiga kaduna basu tsaya ko ina ba sai unguwar sarki gidan mami suna zuwa saka makon suma yan gidan ne mai gadi ya bude masu get suka shiga sukayi parking gaba daya suka fito daga mota suka nufi cikin gidan, mami na kichen taji kamar muryar yusuf na sallama cikin sauri ta fito zuwa falo tana shiga ta gansu zaune cikin fara'a tace aaa bakin nan kun iya bazata daga ina haka cikin jin dadi yusuf ya ce mami daga gida umar yace mami dan lelenki ne yace ya sai yaga maminshi.
Umar ya gaya mata komi yusuf kansa na kasa don kunyar mami yaji sosai Mami tace ba damuwa barima in kira Alhaji ku kwantar da hankalinku komi zaiyi daidai insha Allahu, mami ta daga waya ta kira Abba bugu daya ya dauka mami ta gaishe shi cikin girmamawa sannan yace maryam lafiya dai ko? cikin girmamawa tace yaya lafiya klau dama wata yar alfarma nake nema wurinka game da yarona yusuf takarashe magana cikin dariya cikin kulawa yace kamar me fa ki fadi ba abunda zai gagara ai in sha Allahu, nan mami ta zaiyyana mashi komi cikin fahimta kuma ya fahimce ta tare dayi mata alkawarin next week zai dawo daga malaisia in ya dawo za'ayi komi agama insha Allahu ta gaya ma yusuf yafara shirye shirye shi ma da yan uwanta aba kowa hakkinsa, mami tace nagode yaya Allah ya kara girma ya amsa da Amin sukayi sallama.
Bazan fasa godiya ba gareku masoyan wannan littafi nawa na tun ina karama ina jin dadin yanda kuke nuna mani kauna nima ina yinku irin sosai da sosai din nan.
Labels: Hausa Novel
0 Comments:
Post a Comment
Subscribe to Post Comments [Atom]
<< Home