Wednesday, March 30, 2022

Tun Ina Karama_ 28 to 29

 


                TUN INA KARAMA


Page 28

Mamaki ne ya hana yusuf magana sbd yanda yaga tashin hankali a fuskar hawwa karara, juyawa tayi ta barshi wurin yana tsaye haka ya ganta ta shige part dinta ta rufe. Murmushi yayi cikin ransa yace hawwa a hankali zaki fahimceni zakuma ki san ke kadaice araina, azahiri kuma girgiza kai kawai yayi ya shige part din shi shima batare da ya kara binta ba.

Hawwa na shiga daki fashewa tayi da kuka tana cewa meyasa nayi sabo da soyayyarsa dama abunda umma ke gani kenan taso rabamu? gaskiya bazan iya ganin wannan rashin hankalin ba ace wai mace ta so hallaka ka amma kana cewa zakaje ka dawo da ita alhali ita ko bin ta kanka batayi ba anya akwai adalci cikin wannan rayuwa kuma kace wai kada afada ma kowa, to me kake nufi ne. 

Haka tai tayin tunaninta wanda babu amsa cikinsa hardai ta tashi tayi wanka tayi sallah. Bata iya cin komi shiyasa ta dan sha tea kawai ta kwanta shima sakamakon tana da ulcer kada ta samu matsala yasa ta sha.

A bangaren yusuf kuma shima hakan take saida ya gama komi zai kwanta ya tuna da umar cewa yayi bazasu je gidan su jamila ba yadai kirata awaya yace ta dawo, haka ya dauki waya bayan ya gama komi ya kira jamila, zaune take tana chatting awaya kiran shi ya shigo wayarta cikin tsoro da fargaba take kallon kiran har ya katse. Tsaki yayi ya kara kira har ta kusa katsewa ta daga cikin karfin hali,"hello tace kafin ta kara magana yace"come back our home right now! kafin ta sake magana taji dif ya kashe wayarsa, cikin mamaki da jin dadi tayi ihu wanda har saida mummy tayo dakin da gudu tana fadin "lafiya jamila.

Mummy yusuf ne ya kirani wai in dawo gidan yanzu ta fada tare da rungume mummy cikin jin dadi mummy tace "amma fa ya shammace mu amma ba komi tunda dama mun gama komi kawai ki maza ki shirya ki tafi kinsan ance da zafizafi akan bugi karfe " gaskiya ne mummy bari kawai in tashi to yi sauri kinga 8:30 tayi kije can ki kara shiryawa kinde ji bayanin danayi maki ko? yes! mummy naji amma kinsan nayi mamakin da abunda nayi masa kuma banji ya fada mani komi  ba harda wannan dan kazagin nashi banji komi ba.

 Ke wai an gaya maki mu na wasa ne har yanzu ke yarinya ce ai an riga angama komi ke dai tashi dama inata tunanin munyi waya da daddy dinki yace gobe zai dawo dama kada ya dawo ya sameki  kuma ya fara fada amma naji dadi tunda anyi haka kuma koda kinje ki kwantar da hankalinki ki bashi hakuri kinga dai alamar yana sonki ko?"gaskiya ne mummy bari ki gani"tasahi tayi ta shiga cikin bathroom ita kuma mummy ta fita don ta fiddo mata komi cikin sauri ta gama komi ta fito ta shiga part din mummy haka suka fito mummy tayi mata rakiya har gaban motarta tare da fada mata yanda ya kamata tayi komi haka ta tashi motarta mai gadi naganin haka yace"ga matsiyaciyar nan bari in bude kafin tayi mani rashin mutunci haka ya wangale mata get. Ita kuma dari da tamanin ta fita gidan batare da tunanin komi ba.

Tunda ya kirata bai sake sukuni ba haka ya zauna zaman jiranta, cikin awa daya ta iso gidan shima mai gadin gidan naga ninta ranshi ya baci haka ya bude mata get din ta shiga cikin izza da rashin hankali parking lot ta isa tayi parking ganin duk motocin gidan na nan yasa tayi ajiyar zuciya tace"shegiya neman wurin zama har an dauko mota hmm zanyi maganinki. Bude kofar motar tayi ta dauko abunda tazo dashi ta fito ta  kulle motar bakin kofar ta isa bell din kofa ta taba sau biyu.

















Tasowa yayi  ya bude mata dama tunda yaji zuwanta yana bude mata yaja ya tsaya, ita kuma kakarin shiga takeyi tana tafiya tana cewa yagida ya jikinka"binta yayi da kallon mamaki cikin takaici yace"normal direct part dinta ta wuce batare da ta saurare shi ba.

Shima rufe gidan yayi ya wuce part din shi tare da tunanin hali irin na jamila wato bata ma iya gaishe shi sai wani izza take nunawa lallai jamila kinyi kuskure yanzu za'a fara game din murmushi yayi tare da shafa kanshi ya kara yin balance a kujerar da yake zaune, tabbas kinyi abubuwan daza su sanya in rabu dake amma da sauran lokaci.

Ita ko hawwa bata ma ji dawowar jamila ba ta riga har tayi bacci, jamila ko na shiga sashenta  ta ajiye magungunanta tayi amfani da wanda zatayi ta boye sauran, tayi imani dama ba zuwa zaiyi ba tashi tayi ta kulle part dinta ta nufi nashi. Dai dai falo suka hadu da hawwa ta taso zataje part din shi itama saboda ulcer ta ta tashi kuma maganinta yana part dinsa ka cibus sukayi dai dai kofar shi kalan kallo suka tsaya yi da mamkin juna itadai hawwa bata san ta dawo ba ita kuma jamila tana ganin mai hawwa zatayi dakin sa bayan yasan tana gidan.....?

Page 29

Tsaki jamila tayi, ta shige itama hawwa tabe baki tayi tabi bayanta, knocking tayi "yace mata " yes come in budewa tayi ta shiga cikin sakin fuska ba kamar dazun ba. 

Sallama hawwa tayi da mamaki ya amsa mata sallama shiga tayi"am kuyi hakuri na shigo maku ba lokacin daya dace ba tana magana tana nufar inda ta ajiye maganin  ta juya zata fita, tashi yayi zai bita don yasan tunda har ta fito neman maganinta awannan lokaci yasan ulcer dinta ce ta tashi.

Lokacin da ya fito har ta kusa shigewa part dinta kiran sunanta yayi "hawwa juyowa tayi tana kallon kara sowarsa yana zuwa hannun ta ya kama suka wuce tare.

Jamila kuwa sakin baki tayi tana kallon su yanda har ya bita baima kula da ita ba ajiyar zuciya ta sauke tare da cewa zanyi maganinku indai nice badai kin iya kilbibi ba, too zan kamaki yarinya ko tare aka haifeku sai kin bar mani yusuf.

Koda suka isa part dinta zaunar da ita yayi akan kujera falo yace" hawwa wai me yasa kike son yin wauta da lafiyarki ni na tabbata yau baki ci abinci ba kuma kinsan kina da larura so kike ki jawo mana wata wahalar little baza ki gane abunda ke zuciyata bane game dake nasan damuwarki to amma ki fahimce ni littel wallahi bana yin wani abunda zan cutar dake kuma bazan bari wani ya cutar dake ba amma ina so ki dauka jamila itace kaddaramu ta rayuwa ba kuma zamu iya kauce mata ba to ina so ki tayani neman mafita wurin Allah insha Allahu zamu samu don Allah ki kwantar da hankalinki ki dawo mani da natsuwata ki saurareni ki daina nisanta kaina dake you are my best friend sweet heart , jinjina kai tayi tace"ba laifina bane zuciyata ce ta kasa cire damuwar dake damuna game dakai ina so nima in saba da rashinka kusa dani saboda nasan ba ni kadai bace awurinka amma na kasa wannan hakuri meyasa bazaka ga laifin "so" ba.

 Ni nasan zuciyata tayi rauni akan soyayyarka yaya amm zanyi kokarin danne zuciyata akan komi ta karashe magana cikin rauni irin nata.

Tausayinta pal aranshi, jawota yayi ajikinsa ya rungume yana jin kamar ya maidata cikin jikinsa "kada ki damu lokaci ne zai zo ya wuce zamuyi rayuwar farin ciki ta har abada don haka yusuf ur own babu wadda zata shiga fadarki our only one in my heart, " nagode tace tare da share hawayen da suka zubo mata "me kika ci yanzu?" Na sha tea."ok ina zuwa tashi yayi yaje wurin fridge

ya dauko mata fresh milk ya dauko cup ya zo wurinta ya bude ya tsiyaya mata ya jawota jikinsa ya samata cup din abakinta bata musaba ta bude bakinta tana sha har ta shanye sannan ya ajiye cup din ya dauko maganin sannan ya bata tasha ya kama hannunta ya mikar da ita hanyar bedroom dinta ya bi da ita suna shiga bathroom suka wuce ta wanke bakinta sannan suka fito ya kama hijabin dake jikinta ta ya cire ya zaunar da ita kan gadon shima zama yayi yace"yakamata ki kwanta saboda nasan zaki school gobe daga masa kai tayi "gud to kwanta, gyarawa tayi ta hau gadon sosai ta kwanta tashi yayi daidai kanta ya shafa kanta tare da yi mata light kiss agoshinta sannan yace" have a nice bed rest my own , murmushi tayi tace"tanks. Kashe mata wutar dakin yayi sannan ya fito ya rufe mata dakin yazo falo nan ma ya kashe mata komi sannan ya fita ya kulle part din ya nufi part dinsa cike da soyayyar matarsa arai yama manta ya bar wata jamila adakinsa.

Haka yasamu jamila tana ta cika tana batsewa kallo daya yayi mata ya wuce bathroom jamila tana son yi mashi rashin mutunci amma babu hali saboda tana son cimma burinta haka ta cije ta daure ta basar, yana fitowa ya shirya cikin kayan baccin sa yazo ya kashe wutar dakin ya hau gadon ya kwanta yana kwanciya itama ta kwanta batare data ce masa komi ba.






 









kowa da abunda ya ke sakawa a zuciyarsa can dai taga shirun tayi yawa kuma tasan ba bacci yakeyi ba haka nan ta share ta matsa kusa da shi ta rungumesa ta baya jinta haka yasa ya juyo shima ya rungumeta sauke ajiyar zuciya tayi da alama tayi missing din shi cikin jin dadi ta cigaba da aika masa da sako shima yana maida mata haka suka cigaba da romancing din juna kamar zasu cinye juna sai da ya tabbatar ta kamu sosai babu abunda take jira sai sex takai karshe so take kawai taji shi cikinta amma ya tsaya bata lokaci. Murmushin mugunta yayi sannan ya tamke fuska ya kunna wutar dakin yace"mata tashi ki bar mani daki cikin razana ta juyo tace "what!!!!.

contact-form


Labels:

Monday, March 28, 2022

(Cancer) Guide for Effective Program - WHO



   WHO Guide for Effective Programmes


The WHO guide is a response to the World Health Assembly resolution on cancer prevention and control (WHA58.22), adopted in May 2005, which calls on Member States to intensify action against cancer by developing and reinforcing cancer control programmes. It builds on National cancer control programmes: policies and managerial guidelines and Preventing chronic diseases: a vital investment, as well as on the various WHO policies that have influenced efforts to control cancer. 

Cancer control aims to reduce the incidence, morbidity and mortality of cancer and to improve the quality of life of cancer patients in a defined population,







 




through the systematic implementation of evidence-based interventions for prevention, early detection, diagnosis, treatment, and palliative care. Comprehensive cancer control addresses the whole population, while seeking to respond to the needs of the different subgroups at risk.

COMPONENTS OF CANCER CONTROL

Prevention - of cancer, especially when integrated with the prevention of chronic diseases and other related issues (such as reproductive health, hepatitis B immunization, HIV/AIDS, occupational and environmental health), offers the greatest
public health potential and the most cost effective long-term method of cancer control.
 We now have sufficient knowledge to prevent around 40% of all cancers. Most cancers are linked to tobacco use, unhealthy diet, or infectious agents (see Prevention module). 

Early detection - detects (or diagnoses) the disease at an early stage, when it has a high potential for cure (e.g. cervical or breast cancer). Interventions are available which permit the early detection and effective treatment of around one third of cases (see Early Detection module).

There are two strategies for early detection:


- Early diagnosis often involving the patient’s awareness of early signs and symptoms, leading to a consultation with a health provider – who then promptly refers the patient for confirmation of diagnosis and treatment;















- National or regional screening of asymptomatic and apparently healthy individuals to detect pre-cancerous lesions or an early stage of cancer and to arrangement referral for diagnosis and treatment.

Treatment aims to cure disease, prolong life, and improve the quality of remaining life after the diagnosis of cancer is confirmed by the appropriate available procedures. The most effective and efficient treatment is linked to early detection programmes and follows evidence-based standards of care.

Patients can benefit either by cure or by prolonged life, in cases of cancers that although disseminated are highly responsive to treatment, including acute leukaemia and lymphoma. This component also addresses rehabilitation aimed at improving the quality of life of patients with impairments due to cancer (see Diagnosis and Treatment module). Palliative care meets the needs of all patients requiring relief from symptoms and of psychosocial and supportive care, particularly those with advanced stages who have a very low chance of being cured or who are facing the terminal phase of the disease. Cancer and its management have emotional, spiritual, social and economic consequences for patients and their family members.

For them, palliative care services addressing their needs from the time of diagnosis can influence their quality of life and their ability to cope effectively (see Palliative Care module). Despite cancer being a global public health problem, many governments have not yet included cancer control in their health agendas.




 






There are competing health problems, and interventions may be chosen in response to the demands of  interest groups, rather than in response to population needs or on the basis of cost effectiveness and affordability. Low-income and disadvantaged groups are generally more exposed to avoidable cancer risk factors, such as environmental carcinogens, tobacco use, alcohol abuse and infectious agents.

These groups have less political influence, less access to health services, and lack education that can empower them to make decisions to protect and improve their own health.

Enter your email address:

Delivered by FeedBurner



contact-form

Labels:

Friday, March 25, 2022

4 Part On Your Body Showed The Sign And Symptoms Of High Level Of Diabetes - WHO



  Test To Avoid Severe Impact On Your Body





Your body is structured in such a way that the glucose sugar produced in the body is broken down to produce energy. In this way, you’re supplied with energy to do your work, while your blood sugar level remains normal. However, in some conditions, glucose can be utilized by the body, which leads to an abnormal increase in blood glucose level called Diabetes.

Diabetes has become prevalent in our society. Although it can be treated or brought under control, it is still very pertinent that you understand the health implications of not paying close attention to your body. Diabetes presents so many health complications which you need to avoid. Therefore, maintaining a healthy lifestyle is key.

Because of increased cases of diabetes in our modern world, it is important to know the sign and symptoms that diabetes presents.





 









This helps you to protect yourself as early diagnosis and treatment are key to the management of diabetes to avoid triggering health complications.

According to Healthline.com, MedicalNewsToday.com, and WebMD.com, diabetes usually presents pains moderate to severe pain in different areas of the body, which can help in early diagnosis and treatment.

 Therefore, you need to pay close attention to your health and look out for the signs to take proper actions. Below are the areas you should look out for:

    Pain in your join

It is normal to feel joint pain sometimes due to stress or hard work, but when you feel such pain without any stressful activity, you need to pay close attention to it. Diabetic pain in the joint occurs when increasing the level of sugar in the blood harms the nerve fibers, causing joint pains. It is usually referred to as diabetic neuropathy.


      Pain in your muscles including muscle                  cramps















Due to muscle wasting mostly witnessed in cases of chronic diabetes, muscle pain develops. This may be localized in muscles of the leg and hands, and can also trigger muscle cramps.

    Pain in arm and leg

This is usually linked to diabetic neuropathy, a condition developed due to lesions of nerve fibers in cases of increased blood sugar levels. The pain is usually mild but progresses gradually to severe pain.

       Pain in your shoulder

According to diabetes.co.uk diabetes can trigger frozen shoulder, also called adhesive capsulitis. This is triggered by the presence of glucose in the collagen fibers around the shoulder.

 Thus sticking the neighboring collagens together. It causes pain and inflammation around the shoulder area.

Endeavor to meet your doctor if you experience frequent pain in these areas discussed above. In addition, ensure that you have your blood sugar level checked, at least once every month. 

Labels:

Thursday, March 24, 2022

Tun Ina Karama 26 to 27



            TUN INA KARAMA

Page 26

Hankali tashe ta nufi yusuf! cikin hanzari ta isa garesa yana dafe da inda jinin yake zuba. ita ko jamila na ganin hawwa ta taho da gudu yasa tayi saurin tsallake sa ta murda key din kofar ta fita a firgice ta fada mota ta bar gidan gabanta na faduwa tana cewa Allah yasa dai ba mugun ciwo ta ji masa ba.








 










Hawwa naganin halin da yusuf yake ciki ta kara fashewa da kuka ta tsugunna ta rungume shi tana kuka ko ba ba'a sanar mata ba tasan aikin jamila ne ganin jinin bai tsaya ba yasa ta tashi da gudu ta koma part dinta ta dauki wayarta ta kira umar bugu daya ya daga jin muryarta yasan ba lafiya "natsu kiyi mani bayani little waye ba lafiya? cikin kuka tace" yayane jamila ta fasa ma kai gashi nan kwance jini na zuba. What, jamila kashe wayar yayi kawai ya nufi gidan yusuf dama yana hanya ne zaije kai wani sako da daddy ya aike shi.












Ganin ya kashe wayar ne tayi sauri ta zira jallabiya da hijabi ta shiga bathroom ta wanke jinin da ya bata mata jiki ta fito da sauri rike da wayarta da tashi daidai shigowar umar shima nufarsa yayi inda yake kwance cikin jini don ya bugu sosai ca kumarsa yayi bai damu da jinin jikinsa ba yana girgiza shi yana cewa "brother wallahi idan har wani abu ya sameka bazan bar jamila ba haka ya sungumi dan uwansa hankali tashe ya fito dashi zuwa mota itama hawwa ganin haka yasa ta bishi da gudu ta shiga motar gudu umar yakeyi har ya kawo Alheri hospital wanda dama shine asibitin families dinsu haka ya isa cikin tashin hankali dama yayi waya da doctor din yana isa suka nufi kansa suka dauke shi sai emagency nan da nan likitan yashiga duba shi tare sauran nurse din hakayayi nasarar cire masa kwalbar da tashige masa a goshi tare dayi masa dinki saboda ta huda shi wurin har yayi rami.













Haka dai aka gama mashi komi aka kaishi dakin hutu, likitan na fita su umar suka tashi suka nufo shi " umar yace yaya doctor? murmushi yayi ya dafa kafadarsa yace" babu damuwa umar muje office haka suka bi doctor har office suna shiga ya nuna masu wurin zama suka zauna sannan doctor yace"bakomi umar yayi sa'a wuri dayane kwalbar ta shige sosai kuma an cireta anyi masa diki wanda dole ne yasamu hutu na wani lokaci koda na sallameku kuma akwai magungunan da za'a nema zan rubuta maka su yanzu kuma idan yayi 3 days zan kwance masa dinkin ana dressing din wurin, amma wai umar sister dinku kuwa she is very stupid tayaya zakiyi ma mijinki haka yanzu da da tsautsayi fa ta fasa mas kai ya mutu fa? umar ji yayi kar zuciyarsa zata fashe sbd takaici amma wallahi idan zai ganta yanzu sai ya canza mata kamanni.

 Murmushin yake yayi yace"nidai fatana kada wani abu yasamu brother"ba komi insha Allahu amma you better ku dauki mataki don ba'a san abunda gaba zatayi ba, Allah ya kyauta Amin umar yace.

Ita ko hawwa banda tunanin irin hali irin na jamila babu abunda takeyi, haka likitan yace su bari sai nan da 1hrs zai sallame su daga nan ya rubuta maganin yace umar yaje ya nemo su haka suka tafi da hawwa tare da kwantar mata da hankali.











Bayan sun gama komi doctor ya sallamesu tare cewa nan da kwana uku su dawo, haka sukayi masa godiya suka tafi. Gaba daya motar babu mai magana saboda kowa da irin tunaninsa akan jamila haka suka isa gida mai gadi ya bude masu kofa tare dayi ma maigidan nasa Allah ya kyauta don yaji komi kuma shima yayi tir da halin jamila.

Suna yin parking hawwa ta fito ta bude masu gidan shi kuma umar ya kama yusuf suka shiga ciki yakai shi har part din hawwa sannan ya nuna ma hawwa yanda maganin yake sannan yace shi zai koma sai da safe dare yayi sosai "yusuf yace bros nagode Allah yabar zumunci." ba komi umar yace Allah ya baka lafiya sai na dawo da safen haka sukayi ban kwana hawwa ta biyo shi ta rufe gidan shi kuma ya shiga mota ya nufi gida cike da takaici aransa.

Jamila ko na fita bata zame ko ina ba sai gidansu tana shiga tayi parking ta fito ta shiga cikin gidan bata zame ko ina ba sai part din hajiya mariya tana shiga ta sameta sai hada mata magungunan takeyi cikin tashin hankali tace mummy na pasa masa kai.

















cikin tsoro tace"garin yaya jamila! zakiyi wannan danyen aikin? wallahi mummy hanani fitowa yayi shine nima na aikata hakan, "kash! amma ke banza ce to yanzu ai kin lalata komi sai ki zauna mu nemi mafita zuwa safe, " ai dole mummy daddy dai bashi nan ko? don shima yanzu naga kamar ya fara bin bayansu Abban yusuf."ke don Allah kyale shi can da munafurcin su kije ki kwanta bashi gari "to mum nagode.

Hawwa na dawowa wurin yusuf ta zauna tace" yaya bari in hada maka tea kasha kafin kasha magani ko, ta tambaye shi cikin damuwa tausayinta na fa aranshi yarinya karama amma ana sanya mata damuwa da yawa why ya tambaya a zuciyarsa, azahiri kuma murmushi yayi yace"duk yanda kike so sweet heat zanyi, murmushi tayi tace to hak ya kamata tashi tayi  ta wuce kitchen ta sanya mashi ruwan zafi tare da warming din kazar da suka zo dashi don su duka babu wanda yaci komi in banda cinye juna da sukayi wanda yasa har jamila tayi masu wannan rashin mutunci.

Haka tayi komi ta dawo ta zauna kusa dashi tana bashi tea din yana sha ita kuma tana ci kadan don ita kanta komi ya fita aranta amma bata so taga yanada damuwa aransa ita dai fatan ta Allah ya bashi lafiya kafin tace komi. Bayan ta gama ne ta taimaka mashi ya shiga bathroom yayi wanka tare suka gama komi suka fito haka ta shirya shi cikin kayan baccinsa saida ta tabbatar ya kwanta sannan itama ta hau bisa gadon ta kwanta tare da rungume shi ta baya juyowa yayi yana mamakin yanda ta canza duk wannan kunyar ta ta ta cireta shima murmushin jin dadi yayi ya kara rungume abinsa ko ba komi ya samu natsuwa aransa, sai muce Asuba ta gari masoyan juna.












Washegari da safe bayan sun gama komi ta bashi magani suna zaune a pallor tayi pillow da cinyarsa shi kuma yana wasa da kalabar dake kanta shi kansa wani dadi yakeji aransa yanda yaga bata damu da abunda ya faru ba bare ta tambaye sa me ya faru tsakaninsa da matarsa. Ba zato taji yace"little amma ina fatan babu wanda yasan me ya faru ina nufin su umma.















 


ariya tayi tace"babu wanda yasani, "good house wife haka ake so mace ta rinka rike sirrin cikin gidanta kuma kada ki damu da abinda jamila takeyi with time kinji ko?" Naji yayana kuma insha Allahu zanyi yanda kace"Allah yayi maki Albarka "Amin dear ta amsa masa tare da kara shigewa jikinsa.

Basu dade ba umar ya shigo duba shi hawwa bayan sun gaisa ne ta tashi taje ta kawo ma shi lemu da ruwa, yusuf ne yace" freind ina so ka rakani in maido da jamila, cikin razana umar ya mike tsaye yana nuna shi da ya tsa zaiyi magana sukaji faduwar tiren da hawwa ta dauko da lemu da glass cup din data dauko suka fadi kasa suka fashe saboda jin furucin da hawwa taji yusuf yayi na zuwa dawo da jamila, gaba daya suka juya tare da ganin hawwa bata tsaya ba sauraren komi ba ta juya da gudu tana kuka.

Page 27

Tana shiga daki tasa key ta fada kan gado ta fashe da kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro, yusuf binta yayi a kidime yana kiran sunanta amma yana isa kofar yaji ta sanya key, komawa yayi wurin umar wanda tunda yazama kamar an dasa shi saboda mamaki yazama kamar status.

Kaga irin abunda nake nuna maka yusuf, yanzu ace kai bazaka iya hakuri da jamila ba saboda sun gama dakai sun maida ka wani wawa saboda da Allah kanayi ma yarinyar nan adalci kuwa? gaskiya yusuf zan fidda hannuna akan wannan badakala taku don bazai yiwu ba kullum problem's yaki karewa tsakaninku kai kuma kullum kalmarka bata wuce revenge zakayi taking ba kuma har yanzu kaki gamawa da al'amarin ba.

Umar kasan bazan boye maka komi ba arayuwata ba to wallahi ban taba son jamila koda da second daya ne idan ba don asiri ba kuma gaba daya mun san haka to jamila tayi mani abubuwa da yawa arayuwa infact ma ince maka ban taba samun mutumin da ya musguna mani ba arayuwa irin jamila idan har na rabu da jamila salun alun to gaskiya banyi abunda ya dace ba amma ina so in nuna ma jamila ita bata isa ba arayuwa duk abunda take takama da shi ina so in raba ta dashi in nuna mata ita bata isa ba kuma bazata iya samun digo araina ba na soyayyarta kuma ina so duniya tayi mata kunci, ina so in azabtar da rayuwarta har sai ta wulakanta sannan inyi mata mai gaba daya zan dasa mata ciwo a zuciyarta wanda har ta mutu bazata daina jin sa ba.







 









Amma hakan bazata samu ba har sai mun zama clothenings da ita don haka ina so ku bani lokacin ku fahimce ni babu komi araina intentionally nayi maganar nan dama ina so hawwa taji don inga reaction dinta kuma nagani zanyi handle din komi ya kara she mgn yana kallon umar sosai.
Ajiyar zuciya umar ya sauke tare da jinjina kai alamar gamsuwa "to amma yusuf taya ita hawwa zata tabbatar ba sonta kake ba?" Yes ina so hawwa ta kwaci kanta wurin jamila tacire tsoron da takeyi mata arai kamar yadda nabila ta bata shawara kuma naga ta dau hanyar yin hakan, kuma ina so ita jamila tasan hawwa ita kadaice macen da nake so a zuciyata duk da ta kasa gane hakan har yanzu zan bita akan asirinta na ta siri har sai nakai inada zamu fara game din daga nan zata fadi kasa warwars daga ita har uwarta."to shikenan amma you have very careful about her "insha Allahu freind." Amma ba yau ba kaje ka lallashi littel. 

Yes wallahi umar tunda ta kulle daki bazata saurareni yanzu ba "to yanzu kasan ya zamuyi?" Ban sani ba umar."nabila zan kira tace mata zata zo yanzu na tabbatar bazata cigaba da fushin ba har kasamu ka fahimtar da ita komi cikin hikima."gud idea freind.

Koda umar ya kira nabila ya fadi mata ga abunda yake so tayi ta amsa da to kuma bata kawo komi aranta ba sannan yace mata bai so abarta ita kadaine tunda zasu fita da yusuf ne, koda nabila ta fada ma umma sakon umar na zuwanta gidan hawwa bata hanata ba don itama tasan hawwa tana bukatar wani kusa da ita tunda jiya ta koma, umma tace ma nabila idan kin shirya ki tafi a motar hawwa saboda abar mata abunta can nasan ai kun kusa komawa school"haka ne umma zan tafi da ita dama key din yana hannuna. To shikenan agaisheta amma kada kiyi dare umar ya maido ki gida "to umma ngd.kiran hawwa tayi kamar yadda umar yace ta sanar mata zuwanta hawwa tana da son boye tsakaninta da yusuf shiyasa koda nabila ta kirata bata daga ba saida ta saita kanta sosai sannan ta kirata kuma ita kanta nabila bata fahimci komi ba.

Suna gama samun mafita umar yace su fita kada ma tasame su haka suka fito shi yusuf ga plastar agoshi gidan su umar suka wuce direct suka nufi sashin umar batare da sun yarda Ammi ta gansu ba bare ta tambaya me yasamu yusuf din.

Ita ko jamila tana gida gabanta na faduwa tana tunanin ya zatayi idan kuma an samu wata matsala tsakaninsu amma tayi mamakin yanda har yanzu bataji wani feed back ba kuma tayi tunanin ko hawwa zata fadi ma umar komi kuma shima tasan daya sani da yanzu yazo yayi mata hauka amma bari takara sauraren su iyaka kawai tace masu bada niyya tayi ba tsautsayine kawai tana wannan tunanin ne mummy ta shigo dakin suka ci gaba da kullawa suna kwance wa.

Nabila data zo wurin hawwa bata fahimci komi ba don bata son daga dawowarta tace ga matsala tana so ta fahimci abunda yusuf yake nufi da zaman su, haka suka sha firarsu kamar bata da wata damuwa koda nabila ta tmby ta aunty jamila cewa tayi ta fita hospital tunda ta na tunanin kamar afternoon takeyi haka suka bar maganar batare da tunanin komi ba azuciyar nabila.

Su umar basu dawo ba sai karfe 4:30 suna zuwa suka iske hawwa kamar ba abunda ya faru tsakaninsu koda nabila ta tambayai hawwa me yasamu yaya a goshi cewa tayi koface ta buge shi yayi rauni Allah ma ya kiyaye, umar najin yanda hawwa take kare mijinta azuciyarsa yace lallai yusuf Allah ya baka yar aljannar mata haka nabila ta jajanta masu sukayi sallama suka rako su har bakin mota suka tafi wurin motar ta ta wuce inda nabila tayi mata parking.


















binta yayi da kallo don ita ko sake kallonshi batayi ba tunda su nabila suka fita budewa tayi ta dauki abunda zata dauka ta rufe bata saurare shi ba ta nufi hanyar shiga cikin gidan binta yayi abaya tana shiga tayi hanyar part dinta cikin sauri ya isa gareta ya rike mata hannu juyowa tayi kafin yayi mgn ta daga masa hannu dakata yusuf! cikin razana ya bita da kallo don ko da wasa bai taba jin ta kira shi agaban shi ba kai tsaye....

contact-form

Labels:

Monday, March 21, 2022

Rahotanni Game Da, Yadda Jirage suka Kashe Shugaban ta ISWAP Dake Jahar Borno





Lugudar Wutar Da Sojojin Sama Ta Nigeria Sukayi, Har Yayi Sana Diyar Mutuwar Jagoransu





Bayanai sun ce mai yiwuwa an kashe jagoran kungiyar ta Wanda aka fisani da ISWAP na yankin yammacin Afirka, mai suna Sani Shuwaram.

Rahoton sun ce  shi Shuwaram da wasu mayakan sa ta kungiyar sun rasa rayukansu ne sanadiyar wani hari ta sama da sojojin Nigeria da ke yankin Marte na jihar Borno ta arewa maso gabashin  ta Najeriya. 

Ta shoshin yada labarai ta Nigeria ta bayyana cewa jiragen saman Najeriya ciki har da super Tucano sun yi lugudan bama bamai a yankin da Shuwuram ya kafa sansanin sa.

Bayanai sun ce Shuwaram ya mutu ne sakamakon harbin bindiga da ya samu a lokacin da jiragen yakin suna lugudar wuta suka kai farmaki sansanin ISWAP da ke yankin Sabon Tumbuns na tafkin Chadi. Kafar ta PRNigeria ta ce wata majiyar tsaro ce ta tabbatar mata da kisan Shuwaram.

Shuwaram yana daga cikin 'yan ta'adda da rundunar sojojin sama ta kai wa hari a Sabon Tumbuns kusa da Kirta Wulgo a watan Fabrairun 2022.














 Hare-haren da aka kai ta sama daga bisani sun yi sanadin mutuwarsa tare da wasu mayakan ISWAP da ake yi wa jinya ciki har da Abu Ibrahim al-Hashimi al- Kurayshi, in ji majiyar .

Sai dai kafar ta PRNigeria ta ce bayanan da ta samu sun ce an zabi Mallam Bako Gorgore a matsayin sabon shugaban kungiyar ta ISWAP wanda zai maye gurbin Shuwaram.

Air Commodore Edward Gabkwet, Ya kuma shaida wa manema labarai cewa sojojin sun kashe 'yan ta'adda amma ba a tantance ko su wane ne ba. Ya ce abu ne da ke bukatar a yi bincike kafin a sanar.

A watan Nuwamban shekarar 2021 ne mambobin Majalisar Shura na ISWAP suka nada Shuwaram, mai shekaru 45, a matsayin sabon shugaba kungiyar.

Labels:

Thursday, March 17, 2022

Steps On How To Change Your Blogger Theme



How to change your theme in your blogger website?

1. First go to your website provider i.e your blogger site, go to your left site an click menu.

2. Check your menu and click THEME? After your theme menu opened? Click down arrow below the CUSTOMISE and click RESTORE.

3. After clicking the restore, goto were you downloaded your theme and select it and click APPLY. your are done.










Make sure follows it gently to avoid mistakes, don't Skip any stage, if you have any errors contact me below via contact form or click the allow on notification to get latest update, goodbye.

contact-form

Labels:

Wednesday, March 16, 2022

Matsalar Da Yawan Jin Waka Ko Sauti Ke Kawowa Dan Adam - Dr. Usman Iro



    MATSALAR JIN SAUTI GA DAN ADAM


Hukumar ta ma aikatar kiwon lafiya ta Duniya ta ce matasa sama da biliyan ɗaya ne a duniya ke cikin barazanar gamuwa da matsalar ji sosai saboda yawan jin sauti ko hayaniya ba tare da kiyayewa ba. Dakta Usman Iro Dan Sani, wani ƙwararren likitan kunne a babban Asibitin kunne, hanci da kuma maƙogwaro wato ENT  dake Kaduna, ya shaida cewa, yawan kara ko jin kide-kide musamman ga matasan da ke sanya abin jin sauti wato (earpiece) a kunnesu na da matukar kawo musu illa ga kunnen.












Ya ce "Yawan kara da kide-kide ko hayaniya a hankali suke cutar da kunne ba tare da mutum ya sani ba". Ya ce yana lalata jijiyoyin kunne wanda shi yakan taimakawa ta wajen daukan duk wani karan da kakeji.

Likitan ya ce sanya earpiece a kunne tamkar sanya babbar lasifika ne a cikin kunne, musamman ma idan ana kure karar da kuma dadewa da shi a kunne kamar yadda matasa ke yi, to lallai da sannu a hankali za su ji suna fuskantar matsalar ji ko wata kara da ya auku a gabansu.





Dakta Usman Iro ya ce "Abu mai amfani a nan shi ne barin amfani da earpiece din ko kuma a rinka rage karar idan an sa a kunne.

 Likitan ya kara da cewa ga wadanda ke aiki ko sana'a a wuraren da akwai kara ko hayaniya, to su rika daukar hutu su je su zauna a wajen da babu kara.

Ya ce kamar yadda jiki ya ke son hutu, to shi ma haka kunne ke son hutu don ya ci gaba da ayyukansa batare da ya wahalaba. Cikin wata tattaunawa da aka yi da shi, ya ce kunne abu ne mai matukar muhimmanci sosai, saboda 'Ji' shi ne rayuwa, Dakta Usman Iro ya ce,"Kunne abu ne mai matukar muhimmanci domin ji shi ne rayuwa, ba za a taba hada rayuwar wanda ke ji da wanda baya ji ba".





Likitan ya ce, daga ji ne ake koyan ilimi, ake sanin abubuwan da ke faruwa na yau da kullum sannan da ji ne ake sauran mu'amala. Dakta Usman, ya ce akwai hanyoyin da mutum zai bi ya gane kunnuwansa lafiya lau suke, kamar idan ana yi wa mutum magana da karfi sannan ya fahimci abin da ake cewa ko in ciwo a kunnen ko jin wasu kara ba na yau da kullum ba, ko kuma kaikayi ko fitar ruwa da dai sauransu, to wadannan alamomi ne na cewa akwai matsala a kunnen mutum, Kwararran likitan kunnen, ya ce, "Mutane su daina kwakular kunne ko zama a wajen da yake akwai kara mai yawa da hayaniya, mutane su kiyaye da duk wadannan don lafiyar kunnuwansu" amma sai dai haryanzu al'umma basa jin shawara.





 Ya ce, ga masu dattin kunne, ko mutum bai taba su ba, ma'ana ya goge su ba, da kansu za su fito wajen kunnen wanda har za a iya gogewa. Amma idan har dattin kunnen ya taru da yawa har ya fara sa mutum ba ya ji sosai, to mafi kyawu shi ne ya je asibiti, in ji likitan kunnen.

Sauran karin bayani?


Wadannan bayanai dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake bikin zagayowar ranar ji ta duniya wadda Hukumar Lafiya ta Duniya wato, WHO ta kirkira.

Ana gudanar da bikin ne a duk ranar 3 ga watan Maris na kowace shekara. An kirkiri ranar ce da nufin wayar da kan jama'a musamman matasa a kan muhimmancin ji da kuma yadda za a kare kunne daga fuskantar duk wata matsala ta ji.





Hukumar Lafiyar ta kiyasta cewa akwai mutum fiye da biliyan daya da miliyan dari biyar da ke fama da matsalar ji a duniya, kusan kaso 20 cikin 100 na al'ummar duniya ke nan. Taken ranar ta na bana shi ne 'Idan mutum na son ya tsufa da kunnensa, to ya kiyaye abubuwan da yake ji.

Labels:

Monday, March 14, 2022

Ko Taya Matasa Zasuyi Game Da Koyan Wankar Gawa - TAHREEM NOOR




Abubuwanda yasa  matasa ke koyon wankan gawa a Birtaniya


An shirya  wani tsari na koyar wa da matasa yadda ake yiwa gawa wanka wato Ghusl a kasar Birtaniya kenan.

Ghusl watau wata kalmar ta britaniya ne yadda ake yi wa mamaci wanka tare da sakamasa kaya da lullube shi da farin ƙyalle, ko kuma Wanda aka fisani da likkafani ne gabanin binne shi, kana daya daga cikin wajiban abubuwa da dana ne da ake yi wa mamaci. Kafin barkewar annobar ta korona, tsofaffin ne masu aikin yiwa gawa wanka sa a cikin fake cikin al'ummar Musulmi suke gudanar da irin wannan al'ada. Amma wasu suna guje wa dan neman kaucewa garkuwa don kare kansu daga cutar korona.
















Yanzu wasu da ake kira Supporting Humanity, wata kungiyar kullawa da masu alhini na gudanar da taron bisa ga matasa masu aiki sa kai don gudanar da wankan gawa a bisa tsarin addinin Musulunci.











 




Jagorar ayyukan kungiyar Tahreem Noor, ta shaida cewa, "yunkurin ya samo asali ne tun bayan barkewar annobar lokacin da adadin wadanda ke mutuwa ya karu" kuma suna "bukatar karin mutane da ke taimakawa da gudanar da jana'izar. Harila kuma yau ana gudanar irin wannan a fadin kasar.

Meyasa ake kira Ghusl a Britaniya?


Kamar yadda addinin Musulunci ya tanada, shi wannan Kalmar ta "Ghusl" wani yanayin daura alwala ne ko wanka da ya ƙunshi tsaftace jiki daga ƙazanta ko Mara tsafter. Akwai wankan kashi daban'daban, kamar na bayan ɗaukewar jinin haihuwa da jinin al'ada. Wanda ake yi wa mamaci Musulmi ana kiransa "Ghusl Mayyit" wato wankan gawa ko wankan wanda yamutu. Galibi dangin suke da jinsi daya da mamacin ne ke gudanarwa. Ya kunshi wanke dukkan sassan jiki da sabullu da ruwa ta hanyoyi na musamman na mutunta gawa.

Muna bukatar akalla masu aikin sa kai bakwai a kan ko wane wankan mamaci, in ji Salma Patel, ta kungiyar Supporting Humanity, wacce ke koyarwa tare da gudanar da wankan Ghusl, kamar yadda ta shaida. Lokacin kullen ta korona, ta bayyana cewa an haramta wa  iyalai da dama yi wa 'yanuwansu jana'iza.













 An bar wa masu aikin sa kai sune kamar ta wankewa tare da yi wa mamata jana'izar a rana lokacin tsananin yaduwar annobar. Takara cewa Mu kan samu kiran waya zuwa a taimaka lokacin jana'iza, amma cikin lokaci kankane muke samu mu aiwatata a yadda ta baiyana.

Lokutan farkon annobar, akwai karancin fadakarwa game da ƙwayar cutar, da kuma ko shin akwai hadarin kamuwa da cutar ta korona daga mamacin. Kungiyoyin Musulmai da dama, da suka hada da Majalisar Musulmai ta Birtaniya da sauran jahohi, sun fitar da ka'idojin da za a bi wajen yi wa mamatan da ake tunanin cutar korona ce ta hallaka yimasa wanka.


















A lokacin, Hukumar Kula da Lafiyar Al'umma ta Ingila ta bayar da shawara kan gudanar da wankan mamaci da yimasa sutura a bisa tsarin da addini ya tanada muddin dai za a cigaba da saka kayan kariya a jiki, da kuma bin dokar bayar da tazara. Cutar ta korona ta yi matukar fi shafar al'ummar kasashen yankin kudancin Asiya Wanda yawanchinsu su sukafi kamuwa da wannan cutar. Dubbai sun mutu daga kwayar cutar, kuma shi ya sa Saffiyah ta yanke shawarar hallatar taron bisa kan wankan gawa a Gabashin London. "Mun rasa rayukan 'yanuwanmu da dama lokacin annobar, kuma zuwa jana'iza da kuma rashin sani me za ka yi wani abin a tashi tsaye ne,'' ta ce.

Daya mai hallatar taron, Khadija, mai shekaru 23, na ganin yana da matukar muhimmanci a koyarwa da matasa irin wannan tsarin saboda, in ji ta dan zai taimakawa alumma. "Muddin ba mu koya ba, wa zai rika wanke gawawwakinmu ta wannan hanyar. Mata (90) ne suka hallarci taron bitar mata Musulma a Cibiyar Belgrave Community Centre da ke Gabashin London.















 An nuna musu hanyoyin yi wa mamaci wanka da kumma sutura a jikin manyan 'yartsanoni . Summaya ta bayyana cewa ba ta san cewa ana rufe tsiracin gawa ba da tsumma lokacin wankan, saboda a matsayinta da matashiya Musulma ta damu "game da tsiraici bayan mutuwa.

Mata, matasa da suka hallarci taron, sun bayyana cewa sun karu sosai da koyarwar, kuma suna jin cewa wannan wani bangare ne na addininsu kuma sunyi farinciki da wannan taron da karin illimi.

Farzana ta bayyana abubuwan da ta koya da cewa "A duk lokacin da mutum ya mutu ana kiransa gawa - ka rasa sunaka, da matsayinka, da komai naka Duk wani abin da kake dashi a duniya za a mance dashi sunanka yazama gawa injita.















Kungiyar Supporting Humanity ta ce annobar wata ''matashiya ce'' lokacin da tsofafi suka kasa gudanar da aikin, kana tana kallon haka a matsayin wani sabon tsari ga matasa da za su bayar da gudunmowa a kai a cikin al'ummarsu.

contact-form

Labels: