Addu'ar Neman Aure Ga Mace Ko Bazauwara? Da Kuma Wacece Mace Tagari? Yaya Ake Gane Su....
Kuma bayani ne game da "wacece mace ta gari, kuma yaya ake ganesu ko kuma yaya Suke har idan namiji yayi ido biyu da su.
- Daya daga ciki shine, idan har mace tazo tayi ido biyu da namijinta a lokacinda yadawo, to zai ji wani iri a jikinsa harwani lokaci zai ji a jikinsa wani iri kuma zai ji jikinsa zai yi sanyi.
- Kuma zakaga tana gaggawa a bisa duk abinda mijinta yagayamata tayi to zakaga tana rawanjiki in ba har tagama ba to hankalinta ba zai kwantaba sai har ta gama.
- Itace Wanda har idan taga hankalika yatashi to baza ta iya zamaba, ko kuma idan ta ga kamar ta baya maka rai sai tayi kokarinta ta ga zuciyar ka yayi haske.
- Zakaga ba ta wasa da addini Kunlun zakaga tana yawan yin nafila da sauran ibadu.
- Zakaga bats wani wasa da duk wani hakkin namijinta Wanda Allah ya dauramata.
- Kuma duk wani sirrin mijinta ba zata bari wani yasaniba, duk wani hiranda ta yi tare da mijinta baza ta taba wani yasaniba ko da kawayentane, dan yawancin mata duna gaya was kawayensu duk abinda sukayi ta wajen kwanciya, amma mace tagari baza ta gayamusu komai game da gidanta ba sai dai ayi hirar wata rayuwa kawai amma banda na aure.
- Kuma itace mace a duk lokacinda mijinta baya gida, to baza ta taba leka ko bakin kofaba da kuma kiyaye duk wani dukiyarsan da yabari da sauransu.
- Ita ce kuma tana kiyaye da duk wani al'amarin gida game da kamar yaranda suna gabanta ko da ba nataba ba zatayi musu babbanciba dan kakkinsu yana wuyanta da sauran hakin da yakrr wuyanta.
- Kuma ita wanda take girmama iyayen mijinta kamar nata. Kuma tana taimaka was yanuwan mijinta batare da wani ba chin rai ba.
- Ita ce wanda zakaga tana zama da kishiyarta da makwabtar su bawani abinda yake shiga sakaninsu kamar fada da sauransu.
WANNE MIJI NAGARI.
Yawanci a rayuwa idan kunduba yanayin rayuwa game da dan adam, amma yawancin zakaga ana cewa Allah yabaka mace nagari amma baza kaga ana kiran namijiba, to wai me yakefaru sai ace Allah yabamu mace nagari. To bari muga meyake sa a San namiji nagari:
- Nafarko shine zakaga yana kulawa da iyalansa towo da miya a ko taina ciki da wake.
- Kuma yana yimusu ishesshen sutura ga su har idan zai yi ma Kansa sutura to Shima sai yahada da su gaba daya baza I so Kansaba.
- Kuma shine namijinda yakan yi hakuri ga ko me yasamesa ko da na bacin rai ma sai kaga baya nuna fushinsa.
- Namiji shine kuma wanda zakaga lokacinda ya aure wanda yakeso sai kaga bayan anyi auren sai kaga yafara sonta feya da ka min ya aureta kuma zai yimata wasa kaman yaro yana sa mata abinci kamar yarinya karama.
- Kuma yazam yana da kishin matarsa, duk wanad baya kishin matar sa to wannan ba miji na gari bane.
- Kuma yazama ya dauki aure a masayin ibada, ba wai kai ya dauki aure wasa kokuma yana wasi wasi da shiba.
- Yazama ya dauki matarsa ita ce abokiyar wasan sa, kuma abokiyar hirarsa, kuma kazama mai yimata zoliya a ko da yaushe dan faran ta mata rai yakan sa ko da yaushe tana nemanka ta ganka.
- Miji nagari baya zagin matarsa, kuma ko da bayan idonta baya zaginta, ko da wani abu yafaru da shi da ita, subiyu kawai a sakaninsu za su sassanta ba wanda zai ji daga waje.
- Shine wanda yake zama da iyalinsa a cikin farinciki a ko da yaushe ba wani zalinta ko cin mutunci.
- Shine a koda yaushe idan matarsa ta bashi shawara zai duba yagani har idan shawaranta yai, zai amfanidashi ba wai kawai idan matarka ta baka shawara sai kayi banza da shiba.
- Kuma baya yiwa matarsa karya, kuma a koda yaushe yakan gaya mata gaskiya ba karya.
- Kuma a koda yaushe, yana baiwa iyayen matarsa daraja kamar yadda yakan bawa iyayensa.
- Kuma yan'uwanta, ya dauke so tamkar danginsa ne, ba wai kawai sai yan'uwansa ba, kowa nashine har idan yana da abin hannu har idan yana taimakawa nashi, to sai ta taimakawa ita ma nata, to shine wannan na gari.
- Kuma kowane namiji nagari, yakan yabon matarsa koda shekarunta yazama yaja bai wai sai ka juyemata baya ba dan ta sufa, zai yi kokari yaja ta jiki dan yanuna mata fa har yanzu babu kamar ita.
GAME DA NEMAN AURE MACE
- Allahummah Swalli Ala Muhammadin wa'aali Muhammad. Kayishi kafa (100) lokaci daya
- Ya Hayyu Ya Qayyum. Shima so (100)
- Allahummah Shaafiy Kulla Mareedh. Shima sau (100).
- Assalamu Alaiki Yaa Zainab Binti Amirul Mumini. Shima sau (100).
SIRRIN SAMUN MIJIN AURE A RUBUTUN "SURATUL MARYAM"
SIRRIN SAMUN AURE TA HANYAR SADAKA DA "DABINO"
SIRRIN TSAYAR DA MANEMI GA MACE
Za a yi wannan rubutun ne a ranar Jumma'a, sai ta ajiye sai ranar lady ta yi wanka da shi amma ba wai a wurinda akwai najasa ba, in har bazata iya ba, sai ta bayar ayimata wannan addu'ar sai tayi wanka dashi, amma sai ranar "La'hadi" zata yi wanka dashi, bayan tagama wanka dashi kar ta goge jikinta sai tayi wannan addu'ar ta "Suratu Yunus" ( Aya 81 zuwa 82) ko har idan bazata iya ba, sai ta samu wani yayi mata (Kafa Bakwai) lokaci daya
In sha allah idan aka yi wannan addu'ar, za a samu biyan bukarta da gaggawa, har idan aka samu masala to sai akara mai maita wannan addu'ar sau uku kuma wannan addu'ar an sha yinta kuma ansamu nasasara.
Labels: Hausa