Sai Na Aureta Ko Baka Saketaba
ABDULLAHI DA KAWUNSA
Abdullahi ne da wani wanda ake cemasa "Kawu" sunyi wani karamar hira ne amma sai wannan hirar tazama da gaske sakamakon kawu yacewa Abdullahi "Kasaketa in aura" a cikin hira, bayan sungama hira da abdullahi sai yacemsa bari zai tafi wajen buga kwallo sai yayi sallama da shi Abdullahi.
Bayan ya iso gida sai yayi sallama baiji an amsa masa wannan sallamar sa yayiba, sai yashi cikin daki sai yaga "Safina" bata cikin daki, yakara damka ihu Sakina!!! Sai yaci shuru, sai zuciyar ya sinki sai yafito waje yana tambayan makobcinsa ko ta shiga zuwa ciking gidansa, sai yace a'a matarka bata shigo ba, sai makobcinsa yace lafiya sai Abdullahi yace masa lafiya.
Sai Abdullahi yafara yintunani akan "Kawu" yana yawan cemasa ko da yaushe sai ya dauke Safina, sai yafara zaton akan ba wanda zai aikata wannan abin sai Kawu.
Sai yaje gidansu Abdullahi yayi sallama akan ko Abdullahi yana nan, sai aka cemasa yafita tunda safe bai dawo ba. Sai yafara tunane akan ina zai sameshi gabadaya Abdullahi hankalinsa yatashi akan wannan yarinyar Safina.
Sai yayi kokarin bari yaje yayi bayani wa jami'an tsaro, bayan ya iso zuwa ofis na jami'an tsaro sai ka wata takaicin bakin ciki da yafaru, sai ga kawu yaturo wani da babbar jaka acike da kudi yashigo zuwa wannan ofishin jami'an tsaro, kamin Abdullahi yayi bayaninsa, sai wannan wanda yana dauke da wannan kudin sai yace DPO ina songaninka anbani sako in baka, sai DPO yatashi yazo gurin wannan bawan allah, Abdullahi yana zaune yana kallon ikon allah mai zai faru, sai yaga wannan wanda yana dauke da kudin yana was DPO magana akunne amma shi Abdullahi bai San me yake gaya masa ba, amma jikinsa yabashi akan kar DPO ya saurareshe.
Sai Abdullahi dayaga DPO yakarba wannan jakar wanda ke dauke da kudi, sai hankalinsa yatashi yarasa abinda zai ce tunda gashi anrufe baking DPO da kudi.
Sai Abdullahi yace wannan Kawu wane irin mutum ne haka, kuma wane irin azzalimine wanda bai da imani a zuciyarsa, Abdullahi yana wannan magana yana zubar da hawaye a idannunsa. Sai Abdullahi Yakima gida dan yayi tunani wace shawara ne zai yi ko wane mataki ne zai dauka game da wannan bawan allah Kawu.
Bayan Abdullahi da yaje gida yace "Wallahi Kawu yajawowa kansa kurar da bazata lafaba, kuma shi da kwanciyar hankali a rayuwarsa yakare har idan bai mayar masa da matarsa Safina ba inji Abdullahi.
Shi Abdullahi yayi shuru da wannan maganar, amma daga bisani sai yayi shawara zai kai magana zuwa kotu dan ta karbo masata matarsa daga hannun wannan azalimin wato Kawu, shi a matsayi kanin ma haifinsane.
Abdullahi yatashi yamiki zarap kamar ansokeshi da allura yagoge idanuwansa ya wanke fuskarsa yarufe ko ina a gidan sai yanufi gidan Kawu, yana kokarin zai shiga sai maigadi yahanashi shiga, yace wannan maigadi nine fa Abdullahi, sai maigadai yace masa angayamasa akan har idan ka karazuwa wannan gidan kar in barka kashiga, sai maigadi yana kofar yarufe kuma yasa kwado yakunle kofar.
Sai abin yabawa Abdullahi mamaki akan wai har yaune zanshiga gidan Kawu za a cemasa ba zai shigababa har mai gadi yana yimasa wulakanci wai har idan shine yazo kar a budemasa kofa, Abdullahi yayi tagumi yatsaya yana ta kallon kofar yarasa abinda yake yimasa dadi ga bakincikin an dauke masa matarsa Safina.
Sai abin ya bawa shi Abdullahi mamaki akan tayaya za a hanashi shigan wannan gidan na Kawunsa, sai yaje tabaya a kawai karamar kofa maigadi yamanta bai kunlle ba, sai Abdullahi ya tura kofar sai ga Kawu yana zaune akan kujera da yakkalla Abdullahi yashigo ta baya, sai yagara murmushi da fuskanrsa da yaga Abdullahi.
Sai Kawu yace wa Abdullahi "Ina fatan kazo da Takardar Tsakin Safina inji Kawu".
Sai Abdullahi yace wannan Kawu lalle kai kacika babban azzalumi, kuma kai babban munafuki ne wanda yake kauda da raba masoya, mai kauda sunnan manzon allah inji shi Abdullahi was Kawu......Kawu yacewa Abdullahi " wai meyasa baka da hankaline zaka dawo har zuwa gidana kana gayamin magana, sai Abdullahi yace, meyasa zaka zo kasace min matata ko dan kasan mahaifina baya duniya ne shiyasa zakayimini haka, kuma dan Kaine ma haifina za saka kazama alwalina za ka aikata mini haka.
Abdullahi yace wa Kawunsa kafitomin da matata ko inkaika zuwa koto akan ka dauke mini matata ka boyeta kuma dole ne zaka fitomin da ita inji Abdullahi.
Sai Kawu yazubawa Abdullahi idanu yana ta kallonsa har yagama fada abinda yakeso a zuciyarsa, sai Kawu yace Abdullahi karkayi taurinkai dan taurin kai shiyakan sa jaki ya shaduka, shawaran da zan baka, ka amsa kudin da zanbaka kokuma kayi asara guda biyu, karasa matarka da kuma kudin da zanbaka, dan tunda nagan wannan matarka Safina, sonta yashiga mini zuciya har nafara sonta kar zan iya rasa raina game da har idan na rasa Safina, shiyasa kawai nayi shawara in saceta kawai tun kamin abin yayi mini zafi, kuma ko kaki, ko kaso,sai Safina tazama nawa.
Abdullahi zan baka shawara akan kar ka bata lokacinka akan wai kana so ka samu Safina, bari ingaya maka kaji, Safina tariga ta iso Kasar Amurka, nayi shawara ne dan a kai mini ita zuwa can zuwa wani lokaci ko kuma ta dauki wani shekaru nasan dole ne zaka hakura da ita kabata takar dan ta.
Zancen wai zaka kai kara zuwa wajen huku, to ka kai ni nasa kai baza ka ci nasara ba, har idan kanagani zaka ci nasara to zaka iya zuwa ko i'na har idan kana gani zaka yi nasara. Ina mai baka shawara dan lar ka abata lokacinka ka amsa kudin da nace zan baka sai kaje kayi aure, nasan zaka samu wanda har tafi Safina amma kai zun zurutun kana da taurin kai zai sa ka rasa duniya, ina mai kara ba aka shawara ka amsa wannan kudin kayi tafiyarka.
Sai Kawu yajuye baya ya shiga gidansa, sai mai gadi yace ma Abdullahi dan allah kayi gaba zamu bude kofa ga masu amfani dan allah ka bada hanya sai mai gadi yayi wa Abdullahi Gwallo yashiga gida kayanshi. Wannan shine karshen bayani, assalamu alaikum.
UWAR MATATA WAI DOLE SAI NAYI AMFANI DA ITA.
Da farko ina daukar wannan Tsangayar taka tamkar wasa. Daga bisa na soma tsintar darusa masu amfani a ciki. Can kuma sai na dawo na natsu ma zama cikenken dalibin wannan Tsangayar. Har ya zamto idan ba kayi postin ba bana jin dadi. Al'amari na da matata ne nake so na bada labari saboda samari wadanda basu yi aure ba su dauke darasi daga ciki.Mun hadu da matata ne a wajen wani fatin bukin kanwar abokina shekaru 8 da suka wuce. Na kamu da soyayyar ta matuka wanda hakan ya rufe mini Idanuwa har bana ganin laifin ta kuma bana so naji an ambata. Kai ko laifin wani na kusa da ita aka ambata sai raina ya baci. bane kuma saboda binciken da aka yi kamin auren mu, sai irin mugayen halayenta da ni na kasa ankara dasu. Kuma ko da an ankara dani bana kula.
Bayan mun haifi dan mu na farko ne a lokacin na soma fahimtar kuskuren dana yi na kin bin shawarar magabata. Sai dai ban iya yiwa kowa magana akan alamun rashin darajar da neke gani a tattare da matata ba. Allah Ya rufa mini asiri ina samu daidai gwargwado. Amma babu wani na kusa dani da ya isa ya moreni muddin tana sane. Babu wani dan uwana da zai zo gidana ta bashi ruwan sha ma bare ace ta bashi abinci. Kai hatta uwata da ake kai mata girki daga gidana sai tayi girkin data san mahaigiyarta bata iya ci. Babu wanda ya iya fadamini wannan matsalar sai har ni na gano da kaina.
Nayi kokarin nusar da ita abun ya faskara. Babu yadda za a jiye kudi a dakina na samesu yadda na ajiye su.Idan nayi magana sai ta manna mini hauka tace ai haka nan na kawo kudin. Da abun ya isheni sai na yanke shawarar karo wata matan. A wannan lokacin mun samu haihuwa karo na biyu. Kuma a wannan lokacin ne kuma na gano irin babban kuskuren da nayi na auro wannan yarinyar. Asiri iri iri babu wanda ba a mini. Ina kwance ina barci zan ji ana wanke mini fuska da rubutu. Hayaƙi agidana babu wanda ba ayi har na cikin ban dakin. Duk wani abu da zan ci ki zan sha to tabbas akwai asiri a ciki.
Duk kokarin ta shine kada na yi wani auren. Haka kuma burin ta na talauce na zauna bani da komai kuma bana yin komai. Ida dai mahaifiyar matata tsohuwar kilaki ce har wannan lokacin danake wannan rubutun bata da aure bugaduniyar ta kawai take yi.
Zancen bin bokaye kuwa kusan duk dangin su Sana'ar tsubbu suke yi. Don haka ne ta daura wannan yarta akan bin bokaye. Ta cusa mata mugayen akidu na son a nakasa ni da kuma yunkurin hana ni aure.
Sau uku uwar matata tana nema nayi zira da ita ina zullewa kuma na kasa bawa kowa wannan labarin. Anakun cewa tayi idan har na amince nayi zina da ita ni da talauci har abada. Kuma arziki na zai bunƙasa. Nacemata yanzu ma na gode Allah.
Na shirya tsaf ana shirin yin bukina karshen wannan shekarar. Har na samu wajen da zan ajiye matar.
Wannan yasa zafin kishin ta da bakin halin ta na gado ya sake kamari. Masifan yau da ban na gobe daban. Wannan makon ya kama mako na uku kenan da ina tashi daga barci sai na ga an kwashe kayan dakina kafkamar an share. Duk wani kayan kudi kama daga talabijjn, su laptop da sauran su har kujerun dakin ankwashi. Ma'ajiyar kudin shi ma an dauke shi cak.
Labels: Soyaiya
0 Comments:
Post a Comment
Subscribe to Post Comments [Atom]
<< Home