Tuesday, March 1, 2022

Tun Ina Karama - 21 to 23


Tun Ina Karama

                     TUN INA KARAMA


Page 21

Ya kirata ya kai 6 times amma bata daga ba a'a to me ya faru ta kirani kuma yanzu na kira bata daga ba why? ya tambaya kansa kuma bashi da amsa ajiye wayar yayi ya nufi bathroom domin ya tsabtace jikinsa don lokacin sallah magarib ya gabato amma tunanin fal aranshi, gashi yayi ma umar alkawalin bazai je gidan ba cikin rashin kuzari yayi komi ya gama ya fito ya sameta still akwance bacci ma ya dauketa cikin jin haushinta da tsana aranshi yaji wani bakin ciki wai me yasa baya iya avoiding dinta idan tazo mashi da bukatarta tsaki yayi, "nikuma nace daga baya kenan yusuf bayan kasha dadi haka ya iso inda take kwance hankalinta kwance ya dubi cinyarta ya bata! Cikin tsoro ta tashi firgigi tace " haba yusuf meye haka? "tashi kibani wuri fita zanyi ya fadi fuskar nan tashi murtuk ba alamar wasa cikin mamaki hali irin na yusuf ya tashi ta tattara kayanta ta fita tana kunkuni.

Kallonta yakeyi acikin ranshi yace jamila kin cuceni babu wani abun birgewa atare dake ranshi ba dadi haka ya dauki key ya kulle ko ina part din shi don yace shi bazai iya bar mata part din bude ba shiyasa ma take zargin ba gidan yake kwana ba amma agidan shi yake kwana saidai kafin ta tashi ya bar gidan.















Tunda dama dai ita ba gwanar girki bace bare ma tasa ran zaici gaba daya babu wani amfana dayakeyi da ita idan sex ba shima sai tayi masa tsibbu kafin tasamu Allah ya tsaremu da bin bokaye Ameen haka ya fita ya nufi gidansu umar suyi sallah kafin su ci abinci don yanzu cin abincin shi ya koma gadansu umar tunda dai bazai samu wurin umma ba bare yayi tunanin zuwa can.

Hawwa tana ganin kiran shi taki dagawa sbd dama ji tayi kawai gabanta na faduwa game dashi kuma tayi mamakin rashin zuwanshi gidan don tasan ko umma ta hana yazo to sai yazo amma tunda ta kira bai daga ba tayi tunanin yana tare da matarshi nan da nan taji kishinsa arai bata so ya gane tana da damuwa dashine shiyasa taki daga wayar yusuf.

Allah ya dawo dasu Abba lafiya ranar yusuf yaje gidansu kamar yadda suka tsara da umar amma umma ko kallo bai isheta ba tadai amsa gaisuwar shi batare da wani sakin fuska ba, bayan angama gaisawa ne tare da ban gajiya tundan kowa cikin murna yake suna daining ne suna cin abinci wanda kowa sai abunda yake so yake ci, shida hawwa kuwa sai kallan kalo sukeyi gani yakeyi ta kara masa kyau ga wani budewa da jikinta yakeyi tayi fresh abunta shi kam da za'a basu dama su kadai da sai ya shanye bakin nan nata don ji yake kamar ya sace ta don sha'awa baya jin feeling don yaga mace amma ita saidai idan bai ganta ba.yana cikin tunanin ne yaji hawwa nacewa umma "umma bari in duba ma Abba farfesun kifin shi wanda zaiyi amfani dashi anjima cikin jin dadi Abba yace" ashe littel bata manta da cimar Abbanta ba.
















Dariya ummah tayi tace ai kaganta nan kullum maganar kenan i'miss my Abba kamar ita kadai ke dashi takare magana ta dungure ta cikin jin kunya ta tashi tabi hanyar kitchen. Da kallo yabita wanda umma na lura dashi kauda kai tayi kamar bata ganshi ba cikin tace nima bari in shiga Alhaji saika shigo "ok to sai na iso.

Tana tashi Abba ya kalli yusuf cikin jin tausayin da'da uba yace Y.B ya naganka so haka? kamar jira yake yace" Abba hawwa "hawwa kuma wani abu tayi maka kuma yasake tambayar sa? girgiza kai yayi yace" gaba daya Abba kunki saurarena akan kuskurena babu mai saurarena cikin fada Abba yace "kai don Allah dakata ince tun kafin in tafi nace maka bazata koma gidanka ba? to yanzu haka ma na samo mata miji yaron wani aminina ne da muke tare dashi a maleysia yanzu haka yana nan zuwa su daidaita tunda ku dai gidan ku na ya hudu ne ba'a haihuwa sai an tsara komi to mu ba haka tsarinmu yake ba, don haka kamar yadda mahaifiyarka ta bukaci takardar hawwa nima ina son ka bata tayi idda sannan wanda ke sonta ya zo neman aurenta.














Don naga alamar zaifi ka sonta da kaunarta.tunda Abba ya fara mgn yaji shi tamkar gunki ai gara Abba ya harbe shi ya mutu kawai yafi masa sauraren maganar nan indai har wani zai auri hawwa gara ya mutu walhi ba zai jure ba, tashi Abba yayai zai bar wurin don ya fara bashi tausayi sosai saurin rike masa kafa yayi yana cewa " yanzu Abba kafi son mutuwata da rayuwata? wallahi bana iya rubuta takarda da hannuna a matsayin saki in ba hawwa saidai ku  kasheni nayarda ya karashe magana cikin kuka mai tsuma zuciya kamar wani karamin yaro.

Magana sukaji daga bayansu ummah nacewa"wannan shine daidai da kai tunda har ka yarda hawwa zata iya zubda ciki da kanta har ka iya barinta a asibiti with condition amma ka tsallaketa ka barta hospital kaida matarka wadda ita ta zubar maka da ciki da hannunta kuma ta karyata kuka yima baiwar Allah sharri yusuf duk bai isheka ba yanzu da da karar kwana daba harda hawwa zata kashe ba.

Don haka yanzu jamila itace matarka dakake alfahari da ita kuma gogga wadda idonta abude yake ita da uwarta sai kuje can ku karata amma hawwa tafi karfinka bata saurari amsa kowa ba ta juya ta fita ta barsu nan shima Abba janye kafarshi yayi yabi bayanta tsugunnewa yayi wurin yaci gaba da kuka ba tare da tunanin komi ba.

Kafadar shi ta dafa tare da mika mashi tissue juyowa yayi yaganta tsaye cikin azama ya mike tsaye tare da rungumota jikinsa cikin tashi hankali yake fadar hawwa zaki rabu dani ki auri wani girgiza masa kai tayi tare da shigewa jikinsa sosai "bazan iya ba yaya amma kuma bazan ja da iyayena ba amma ni na yafe maka cikin kuka itama ta kara she maganar kara matseta yayi cikin murmushin takaice yace hawwa zanje gidan daddy in rokeshi nasan shi bazaya ki taimako na ba cike da gamsuwa ta amsa da to yayana kada kabari suyi nasarar rabamu.

Dago kanta yayi ya hade bakinsu wuri daya ya cigaba da kissing dinta ba tare da tunanin komi a ransu ba, duk abunda yake faruwa tsakaninsu akan idon Abba don shi daya tafi dawowa yayi don ya lallashi yaron nasa amma me sai ya iske su cikin wannan halin ko yanzu ya kara tabbatar da cewa suna son junan su kuma suna da bukatar kulawar junan su.

Ajiyar zuciya ya sauke ya juya cike da farin ciki yana jin haushin kanwar tasa data shigar da rayuwar diyarta mara tarbiyya cikinsu amma ba komi akwai Alla ya furta tare da shigewa part dinsa. Gaskiya ne Abba dogaro da Allah jari romancing din juna sukayi sosai da alama maganar umar hakane ya lura tayi missing din shi sosai shima haka ne don yanzu haka sai yayi wanka don gaba daya wandon shi ya baci sbd making love yanda ya kamata a kujerun daining ko tsoron ummah ta fito basayi dago tayayi yana goge mata hawaye da hannunsa cikin husky voice dinsa yace "i promise you idan baki kwana gidana ba yau to insha Allahu gobe kina gidana saurin dagowa tayi don tabbatar da maganarsa cikin sanyita tace really? murmushi yayi mai kyau ya kara tabbatar mata da hakane, nan ta kara shigewa jikinsa shikuma ya rungume abunsa da kyau. To komi yusuf ya taka yake wannana alkawari oho....?

Page 22

Koda yusuf ya fita daga gidansu gidansu umar ya nufa yana zuwa ya sami umar a bakin get din gidansu zai fita ganin shi ne yasa ya gyara parking din motarsa wanda dama fita zaiyi yana zuwa shima parking yayi kowa ya fito yana welcoming dan uwansa hannu suka mika ma junansu tare da sallama murmushi umar yayi yace"freind gidan Abba zani yanzu nayi tunanin ko kana can? sosa keya yusuf yayi yace"daga can nake bros yanzuma zuwa nayi in sameka muje kankiya.















Kankiya lafiya umar ya tambaya shi?"yes to lafiya kam da sauki wannan karon hajiya kakace kawai zata taimakeni "amma ai dazun mun fara maganar da daddy kuma nasan zaiyi komi umar ya fada cikin kulawa, kayi hakuri brother mu gani" wallahi idan bazakaje ba ni inyi tafiyata yusuf ya fada cikin fushi! a'a yi hakuri friend ni na isa ince ban zuwa ai mu wuce na kira Ammi in sanar mata.

Kiran mai gadin yayi yace mashi ga key din motar nan zan fada ma nabila tazo ta shiga da ita gida."to ranka shi dade adawo lafiya "Amin ya amsa tare da bude kofar motar yusuf ya shiga suka dau hanya sai kankiya kan tsiyar katsina.

Ba wani lokaci mai tsawo suka dauka ba suka isa kankiya, suna zuwa basu zame ko ina ba sai gidan hajiya kaka suna zuwa mai gadi ya bude masu kofa suka shiga, bayan sunyi parking ne suka fito da fara'a suka gaishe da mal sale mai gadi cikin mutunci da mutun tawa, wucewa sukayi zuwa cikin gidan suna shiga da sallama cikin murna kaka ta amsa masu tare da cewa" yau kuma kun tuna da ni na ganku haka ko dariya dukayi gaba dayansu tare da zama yusuf yace"to ba ance kikoma birni ba kin ki kina nan kauye kina cin dawa da gero eh din ai ku baku da abinci sai shinkafa sai kayan kwalaye da gwan gwanaye umar yace da kina cinsu da yanzu kin kara girma.

















uwaka nace umaru yo ni Allah na tuba ai saidai akabari idan anayin girma ai kin ji ki menene kuma umaru my name is umar bashir mado kuma kema kin sani dariya sukayi gaba daya wanda shi yusuf har isa wurin da take ajiye furarta ya dauko ya fara sha."oni yasu daga zuwa ba'a tambaya sai kawai a dauke ma mutum abu akama sha kaga isuhu ka kiyayeni, ko kula ta baiyi ba umar ne yace ke kinyi baki amma baki basu ko ruw ba. To ai kunsan inda komi yake koni yar aikenku ce takara she magana tanayi dariya.

Kaini yanzu dai me ya kawoku? don da ganin wannan tafiya ba banza ba tunda dai dazun ai munyi waya da iyayenku kuma kowa lafiya to amma ku me kuka zoyi?"yusuf yace walhi indai kina sona to ki ceto rayuwa ta saboda kowa so yake ya rabani da hawwa bai boye mata komi ba ya fada mata, cikin damuwa tace ai ni banga abunda yasa ka kyale jamila ba akan wannan aika aikan datayi saboda Allah umaru nasan da kaine da yanzu kaci ubanta Allah dai yayi wadaran mariya da ta lalata yarinyar nan shi kuma ubanta ba katabus agidan shi kai kuma da yake sakarai ne kaki daukar mataki to ai gashi nan sun rabaka da matar arzuki kai kuma ka kasa zama lafiya.

Tunda ta fara fada babu wanda yace mata komi har ta gama.nisawa tayi tace suma ai basu kyauta ba tunda ai dai ba hawwa tace bata komawa dakinta ba ko? daga mata kai yayi alamar yes, "to kwantar da hankalinka babu wanda ya isa ya hanaka matarka  murmushi yayi wanda yasa har yasa wushiryarsa ta bayyana cikin jin dadi yace shiyasa muke maki Addu'ar nisan kwana haka dai zan barku nan dai suka ci gaba tattauna yanda zasu bullowa alamarin daga karshe dai tace masu su bari sai gobe su taho katsina tare.
















Suna zaune a pallow suna hira domin kaka har ta kwanta wayar yusuf ce tayi ringing ganin su nan my angel ne yasa ya daga wayar tare da tashi yana shigewa cikin bedroom." Hello my heartbit yakake"i'm fine cikin shagwaba kamar tana gabansa tace"nifa na kasa natsuwa banjika ba kuma banji ka dawo ba kuma umma da Abba banji sunyi mani wata magana ba.

Murmushi yayi yace ai nace maki little karki damu komi zai zo da sauki kedai ki bani nan da 24hrs insha Allahu dariya tayi har saida yaji sautinta tace ok my lovely husband cikin jin dadi yace kina ina ne,? ina nan kwance da kewarka to bari in kiraki video call dif ya kashe wayar murmushi tayi tare da kunna data tana hawa online yana kiranta dagawa tayi zaune take kan gado daga ita sai wata yar karamar riga ajikinta ganin juna dasukayi sai kowa hankalinsa ya tashi kusan minti biyu babu maganan can yusuf yayi karfin halin cewa little anya zan iya hakuri da rashinki don Allah ki tausaya mani bani da wani buri da ya wuce naki banso rayuwar mu ta kasance haka ba amma bana kara kuskuren danayi baya ya kara she mgn cikin juyayi"wallahi yaya bana ganin laifinka tunda nasan burin dakayi ma wannan cikin.


















Runtse idonshi yayi yace insha Allahu gobe zan kara ajiyata kuma wallahi bazan kara sakaci akan cikina ba kunya ya bata ta rufe fuskarta haka suka dade suna waya amma bai nuna mata yana kankiya ba son surprised dinta yake so yayi bayan sun gama ne ya fito falo umar yace masoya kai nima dai dole inzo in matsama mami ta bani matata.zama yayi yace kaidai zauna nan kaji da gulmarka.

Yana kwance ya fara bacci yaji karar wayarsa dauka yayi batare da ya duba mai kiran ba ya kara akunnensa ba sallama ba komi cikin fada"tace to na mamajo sarkin mata duk biya maka bukatar da najeyi amma baka kyale wannan yarinyar mai kama da zubin mayu wallahi yusuf kaji kunya ka zauna kaita yi mata ciki. Kafin ta cigaba da mgn yusuf yace ai bawai dadin mu amalar nake ji da ke ba kawai ina rage yawa ne ko kibani kanki ko kada ki bani nothing me "o hakafriend ko to wallahi yusus zaka san kayi dani wallahi sai na rama kashe wayarsa yayi cikin bacin rai ya koma.

Washegari gaba daya suka kama hanya komawa gida harda kaka suna isa katsina gidan su Abba suka nufa.mamaki ne ya cika Abba da yaga gansu tare da mahaifiyarsa itama umma haka ne cikin karfin hali kowa ke yin abunsa gaisheta sukayi sosai cikin girma mawa.

Bayan angama komi ne kowa ya natsu ta sanya aka kira mata Alhaji bello bayan kowa ya hadu ne a babban falon gidan anyi shiru aji abunda hajiyar kankiya zata fada ta bude baki zatayi magana kenan, sai mgnar ta makale sakamakon jin jamila da sukayi tana cewa kaka kada ki shiga hurumin da ba naki ba gaba dayan su juya wa sukayi suna kallonta yanda take shigowa cikin falon cike da rashin kunya da wulakanci....?

Page 23

Cikin mamaki gaba daya wanda ke falon suka juya don ganin jamila Abba aransa yace wannan wane irin bala'ine ke tun karar rayuwar yarana, kowa da tunanin da yakeyi aransa in ka fidda ni dana sume awurin, kara sowa tayi ta rike kugu cike da masifa, kafin ta fara mgn umar yayi karfin hali a hasale ya tashi yaje gabanta ya nunata da dan yatsa yace "cikin tsawa! kibi hanyar da kika fito ki koma inda kika fito tun kafin kiga kalar haukan nawa ke karamar mara kunyace amma rufin asirinki kada ki sake furta koda kalma daya agidan nan, fita kawai! yace tare da nuna mata kofa da hannunsa.
















Tasan waye umar idan tayi sake yanzu zai jibgi banza babu kuma mai kwatarta haka ta juya cikin bakin cikin batayi abunda ya kawo ta ba tafita da sauri tare da banko masu kofar, kaka tace" yau naga abunda ya isheni ni hauwa'u yanzu nan isuhu haka kake zama da wannan shedaniyar yarinyar tanayin yanda taga dama? to tun wuri kasan cewa wannan ba matar mutunci bace ba dolene dije tace bazata baka diyarta ba.

Umar yace"ke kuma granny kada ki kara tunzura mana umma mana.hararar shi kuma tayi shikuma ya sunne kai yana dariya.

Daddy ne yace wannan lamari na jamila ya wuce tunanin kowa saidai Allah ya sawwake, suka amsa da Amin, kaka tace"to ai ni nan banga mata ba yazama dole kuba isuhu matar shi ta koma dakinta kallon hawwa tayi cike da tausayinta tace kiyi hakuri takwara ki koma dakin mijinki kinsan komi na rayuwa kaddara ne to wannan ba abunda zaki rike azuciyarki bane ki kaddara haka Allah ya nufa.

Ke kuma dije bai kamata ki fushi da isuhu haka ba tsaka ninki dashi Addu'a ne Allah ya tsare maki shi daga sharrin wadannan mutane amma ki bar yarinya ta koma dakinta kinji ko.

To hajiya ai magana ta kare yanda kikace haka za'ayi banida wata jayayya Allah ya kyauta gaba, Amin yar albarka " kaka tace Abba da daddy sunji dadin yanda umma take mutunta masu uwa gaskiya suna yabawa da halinta.
















Abba ne yace "to amma hajiya kikara gargadinsa akan yazama namiji agidansa ya kuma tashi tsaye da Addu'a domin ita ce makamin mumini kada ya rinka sanya ma kanshi jamila zata iya mashi wani abu arayuwa yadai bar ma Allah kawai kuma tsaya da kafafunshi don mu kinga bazamu tsaya kullum muna mashi shara aba kuma babu mai cewa ya saki jamila don haka idan zata shiryu Allah ya shiryar da ita.

Amin suka amsa gaba daya sannan suka cigaba da tattaunawarsu ta uwa yaranta don umma dasu umar kowa ya bar falon hawwa da nabila ma sun koma daki.

Anan kaka take cewa " nidai nafi tausayin nabila gaba daya bata biyo halin gidansu ba yanda kasan dije ta haifeta wallahi. Abba yace"shiyasa nake tunanin hadata da umar hada baki sukayi da daddy da kaka wurin cewa masha Allah amma fa kayi tunani Alhaji karami dayake haka take kiransa"ai hjy nasan yar wurin mami ta kd bata da matsala tunda har munyi magana da babanta ya nuna hakan daidai ne ko don a kubutar da yarinyar daga fitinar mariya don mun tabbatar ko mariya tana shakkar umar don shi kanshi uban abun yafara damun shi ya fara gajiya da halin mariya.

Daddy yace indai hakane to Allah ya fara taimakonsa."ai shima gara ku hada mashi biyun  yaje can yayita kaya, dariya sukayi tare da cewa suma zasu fita tashi sukayi tare da sallama suka fita, Umar ko yana can ya tasa yusuf agaba sai zolayarsa yakeyi tunda sun shirya meeting a satin amma yusuf yace ma umar cancelled sai next week don shi idan hawwa ta koma yau shida office sai next week.

Jamila na fita rai bace bata zame ko ina ba sai gidansu wurin mummy tana shiga ko parking mai kyau batayi ba ta fito ta fada cikin gidan hankalinta a tashi ba sallama bakomi kawai sai kiran, mum! mummy! Cikin sauri hajiya mariya ta fito a firgice tana fadin lafiya kike jamila aiko tana isa ta fada jikinta tare da fashewa da kuka cikin "tashin hankali take tambayar diyar tata haka ta zauna tafadi mata korar karen da umar yayi mata da iyayensa basu ce komi ba...?

contact-form

Labels:

0 Comments:

Post a Comment

Subscribe to Post Comments [Atom]

<< Home